'Yansanda Sun Mayar Wa Da Kotu Motocin Da Aka Dauka A Gidan Matawalle – ‘Yansanda
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Mayar Wa Da Kotu Motocin Da Aka Dauka A Gidan Matawalle – ‘Yansanda

Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

byMuhammad
2 years ago
Matawalle

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce ta mayar da dukkanin motocin da ta kama daga hannun tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle zuwa kotu.

Wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan Telebijin na Channels ya yi ranar Asabar da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

  • ‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40
  • Sakarci Da Talauci Ne Yasa Gwamnatin Zamfara Shiga Gidana Sata- Bello Matawalle

“Eh, rundunar ‘yan sanda ta bi umarnin kotu dangane da mayar da dukkan motocin tsohon gwamna Bello Matawalle,” Cewar Kakakin ‘Yansandan.

“Mun mayar da dukkan motocin zuwa harabar babbar kotun tarayya da ke Gusau, kamar yadda nake magana da ku yanzu, babu wata mota guda da ke hannun ‘yan sanda.”

A ranar 15 ga watan Yuni, mai shari’a Aliyu Bappa na babbar kotun tarayya Gusau ya umurci dukkanin jami’an tsaro da ke da ruwa da tsaki wajen kwashe motocin daga gidajen Matawalle na Gusau da Maradun da su dawo da su cikin sa’o’i 48.

Kotun ta kuma bayar da umarnin dakatar da wadanda ake kara a karar da Matawalle ya shigar a gaban kotu daga daukar wani mataki na gaba dangane da lamarin.

Wadanda suka amsa karar sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya da hukumar ‘yan sandan Nijeriya da kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kuma hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC).

Gidan Talabijin na Channels ya ziyarci babbar kotun tarayya da safiyar Lahadi domin tabbatar da wannan umarnin inda ya rawaito cewa motoci 29 ne kawai ke harabar kotun har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

Sai dai majiyoyi sun ce har yanzu wasu motocin na nan a sansanin ‘yan sanda ana sa ran za su isa Gusau a yau Lahadi ko kuma safiyar Litinin.

Sai dai har yanzu tsohon gwamnan bai tabbatar da ko an dawo da motocin ba, har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

A baya dai gwamnatin jihar Zamfara ta ce an kwato fiye da motoci 40 da suka hada da motocin hana shigar harsashi guda uku da kuma SUV guda takwas daga gidajen tsohon gwamnan biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Mata Sun Cancanci Samun Karin Mukamai A Gwamnati — Remi Tinubu

Mata Sun Cancanci Samun Karin Mukamai A Gwamnati — Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version