• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 weeks ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar tarwatsawa da wargaza wuraren haɗawa da rabar da taki na bogi guda uku a jihar Bauchi tare da kamo kayayyakin da ake amfani da su wajen haɗa takin na bogi. 

 

A wata sanarwar da kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya fitar a ranar Laraba, ya ce, sun yi amfani da wani rahoton sirri da suka samu a ranar 10 ga watan Mayu wajen kai samamen.

  • Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Jami’an sintiri na rundunar sun kai ga kama wani mutum Muhammad Abubakar a gidansa da ke Magaji Quarters Bauchi ɗauke da buhun taki na bogi da aka sarrafa guda 6 da kwalaben maganin ciyawa guda 46.

Jabun taki

Labarai Masu Nasaba

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

A wani bincike da aka gudanar a gidansa da ke unguwar Magaji Quarters, an gano katan 38 da babu kowa a ciki na maganin ciyawa iri-iri, buhunan NPK guda 14, buhunan Indorama guda 9, jerikan cokali guda biyar, murhun gawayi, daurin ledoji, da buhunan da ke ɗauke da Ztars da garin lambda.

 

Yayin da ake masa tambayoyi, Abubakar ya yi iƙirarin cewa makwancinsa, Abubakar Umar, shi ma na da hannu a lamarin.

 

A ranar 14 ga watan Mayu, bayan wani rahoto na daban, ‘yan sanda sun kai samame a wani shago da ke kan titin Gombe a cikin garin na Bauchi mallakin wani Anas Abubakar mai shekaru 32. An same shi da buhunan 44.5 na gurɓataccen taki

 

Da ya ke fuskantar tambayoyi, Anas ya amsa cewa na samun kayan kaolin da yake amfani da shi wajen haɗa gurɓataccen taki daga wajen wani mai suna Abdulrahaman Muhammad, ɗan shekara 24 mazaunin unguwar Bakaro.

 

Kazalika, jami’an ‘yansandan sun cigaba da zurfafa bincike inda hakan ya kai su ga kamo wani mai suna Ziya’u Bala, ɗan shekara 27 a duniya mazaunin unguwar Gudum Hausawa, wanda ya yi rakiya wa jami’an zuwa wanin wurin da ake aikin haɗa taki ba bisa ƙa’ida a rugar Natsira da ke ƙauyen Kangere. Wurin mai ɗauke da buhu kusan 100 na gurɓataccen taki.

 

‘Yansandan sun kamo buhun jabun taki guda 44, buhun kaolin guda 100, buhun taki 12, da buhun taki urea.

 

Wuraren hada jabun takin guda biyu da Sama’ila Abdullahi, da Mujahid Abdullahi suke gudanarwa a Natsira da Kangere duk an gano su.

 

Duk wanda ake zargi sun ce suna haɗa takin ne tare da sayar ma wani Abdulrahaman, inda shi kuma yake kaiwa ga Anas.

 

Dukkanin wuraren hada takin na jabu guda uku an tarwatsa da kamo kayayyakin da suke amfani da su wajen haɗa gurɓatattun taki.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Sani-Omolori Aliyu, ya tabbatar da aniyar rundunar na gudanar da masu irin wannan aika-aikar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Next Post

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Related

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

17 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

4 hours ago
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
Manyan Labarai

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

4 hours ago
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
Labarai

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

6 hours ago
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

7 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

10 hours ago
Next Post
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

LABARAI MASU NASABA

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.