Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ta Faru Ta Kare: Buhari Ya Ce Duk Wani Nadadden Jami’in Gwamnati Mai Son Takara Ya Yi Murabus

by
4 days ago
in LABARAI
2 min read
Ta Faru Ta Kare: Buhari Ya Ce Duk Wani Nadadden Jami’in Gwamnati Mai Son Takara Ya Yi Murabus
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Ga dukkan alamu dai ta faru ta kare game da tsame wasu jami’an gwamnatin Buhari da aka nada a mukamai daban-daban a cikin umarnin murabus ga duk mai son tsayawa takara a 2023, da Shugaba Buhari ya bayar a jiya Laraba.

Da safiyar yau Alhamis Buhari ya fitar da wata sanarwar cewa duk wani nadadden jami’in gwamnati da ke shugabantar ma’aikata ko hukuma da yake muradin takara ya yi murabus.

  • 2023: Duk Wanda Ya Yanki Fom Din Shiga Takara Ya Ajiye Mukaminsa —Buhari
  • 2023: Minista Ya Yi Murabus Jim-Kadan Bayan Umarnin Da Buhari Ya Bayar
  • 2023: Zan Shawarci Buhari Da ‘Yan Mazabata Kafin Na Yi Murabus —Ngige

Babban Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha ya rattaba wa sanarwar hannu wacce LEADERSHIP ta samu kwafinta.

Labarai Masu Nasaba

Batanci Ga Ma’aiki: Gwamnatin Sakkwato Ta Sassauta Dokar Kulle A Fadin Jihar

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Sanarwar an aike ta ga dukkan ministoci, shugabannin ma’aikatu na tarayya, babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaron kasa, shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), shugaban Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa ta ICPC, Shugaban Hukumar Yaki Da Damfara Da Kassara Tattalin Arzikin Kasa (EFCC) da sauransu.

Sanarwar ta ce dukkan wani mai son takara da ke kan kujerar shugabanci ta nadi ya yi murabus kafin nan da ranar Litinin 16 ga Mayun 2022.

“Domin kawar da duk wata tantama, wannan umarni ya shafi dukkan ministoci, shugabannin hukumomin gwamnati, jakadu da sauran wadanda aka naɗa a mukamai na siyasa da suke da muradin tsayawa takara.

“Domin ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati yadda ya kamata, dukkan ministocin da abin ya shafa za su mika ragama ga kananan ministocin da ke ma’aikatunsu, idan kuma babu karamin minista a ma’aikatar, su mika ga manyan sakatarorin ma’aikatun.

“Su kuwa jakadodi su mika ragama ga mataimakansu ko kuma babban jami’i da ke ofishin jakadancinsu kamar dai yadda yake a ka’ida.” In ji sanarwar.

Tuni dai tun jiya Laraba wasu ministocin suka yi murabus bayan samun umarnin na Shugaba Buhari.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Sin Ta Kafa Tarihin Cimma Manyan Nasarori A Fannin Bude Kofa Ga Waje

Next Post

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

Labarai Masu Nasaba

Batanci Ga Ma’aiki: Gwamnatin Sakkwato Ta Sassauta Dokar Kulle A Fadin Jihar

Batanci Ga Ma’aiki: Gwamnatin Sakkwato Ta Sassauta Dokar Kulle A Fadin Jihar

by
12 mins ago
0

...

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

by
16 hours ago
0

...

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

by
19 hours ago
0

...

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

by
23 hours ago
0

...

Next Post
Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: