Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Yari Ne Zai Karbi Ragamar Shugabancin APC – Magoya Baya  

by
11 months ago
in LABARAI
2 min read
Yari
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Mahdi M. Muhammad,

Wata kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC sun bayyana cewa, duk da rikice-rikicen da ke faruwa a kan shugabancin jam’iyyar a matakai daban-daban, tsohon Gwamnan jihar Zamfara kuma tsohon Shugaban kungiyar Gwamnonin Nijeriya, Alhaji Abdulaziz Yari na shirin zama Shugaban jam’iyyar APC na kasa na gaba daya.

Da suke zantawa da manema labarai a Abuja ranar Lahadi, mambobin sabuwar kungiyar da aka kafa ta ‘Progress for Yari’ (P4Y) sun sanar da shirye-shiryen fara wani gagarumin farmaki kan mummunar labarin karya da ake shirin yiwa Yari, baya ga tona wasu tsirarun manyan ‘yan siyasa da ke bayan irin wadannan ayyukan na bantanci.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Suka kara da cewa, “APC na bukatar Shugaba na kasa kamar Yari wanda zai iya hada kan mutane domin yin nasara a shekarar 2023, domin yana da matukar muhimmanci a lokacin da muke da irin wannan dabi’ar wacce take matukar biyayya ga APC baya ga samun cikakken karfin gudanar da manufofin jam’iyyar da yi mata aiki a dukkan matakai.”

Kungiyar wacce wakilai uku da suka hada da, Jide Kehinde, Umar Adamu da Emeka Nwafor-Ibe suka wakilta, kungiyar ta tabbatar da cewa, dabaru daban-daban da wasu ‘yan kararrakin kotu da ba su hada da wani hukunci mai laifi daya da aka yanke wa dan takarar na su ba, ba abin damuwa ba ne.

Suka ci gaba da cewa, “ganin yadda labarin karya mara tushe da ake ta yadawa ta hanyar yanar gizo da ke nuna cewa an kame gwal na miliyoyin Naira na Alhaji Yari a filin jirgin saman Kotoka, wasu daga cikin magoya bayan Alhaji Yari na Shugabancin kasa sun yanke shawarar tunkarar wadannan makirce-makirce zuwa gaba.”

ADVERTISEMENT

“Ana kammala shirye-shirye don kaddamar da shirin ‘Progress for Yari’ (P4Y) a duk yankuna shida na yankunan siyasa a duk fadin tarayya, kuma da sannu zaku ji labarinmu da yawa akai-akai,” in ji su.

Suka ce, “ba tare da wata shakku ba, Alhaji Yari ya kasance yana da masaniyar jama’a kuma a koyaushe yana bayyana bukatar ‘yan siyasa su kasance a shirye don ba da sassauci da kuma kiyaye amincin jam’iyya,  kuma babu shakka, kusancinsa da kuma samun dammarsa ga mambobin jam’iyyar a fadin shiyyoyin siyasa shida na kasar nan sun tsayar da shi tuni.”

Suka kara da cewa, “ba kamar ‘yan siyasar da suka fi son makirci ba, Alhaji Yari ya kasance mai son yin sulhu da son zaman lafiya wanda zai zama alheri ga jam’iyyarmu ta APC a matakin jiha da kasa. Bugu da kari, APC na bukatar Shugaba na kasa kamar Yari wanda zai iya hada kan mutane domin yin nasara a shekarar 2023, domin yana da matukar muhimmanci yayin da muke da irin wannan halin wanda yake matukar biyayya ga APC baya ga samun cikakken karfin gudanar da manufofin jam’iyyar da yi mata aiki a dukkan matakai.”

“Dan takararmu baya yin alfahar, kuma ba tare da wata shakka ba yana da babbar dabara da kuma dabaru wajen jagorantar jam’iyyar APC,” in ji su.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Asusun UNICEF Ya Bukaci Gaggauta Sakin Daliban Islamiyyar Da Aka Sace A Neja

Next Post

Kawanyar Da Masu Garkuwa Suka Yi Wa Zazzau Kwanan Nan

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
4 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
6 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
15 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
16 hours ago
0

...

Next Post
Masu Garkuwa

Kawanyar Da Masu Garkuwa Suka Yi Wa Zazzau Kwanan Nan

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: