Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Yaron Da Kishiyar Mahaifiyarsa Ta Yankewa Al’aura Ya Rasu

by Tayo Adelaja
September 11, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammadu Awwal Umar, Minna

A cikin watan shidana bara ne aka zargi Maimuna kishiyar mahaifiyar Buhari Muhammad Awwal Wada da yankewa jaririn dan watanni tara da haihuwa al’aura. Wanda bayan hukumar kula da hakkin yara karkashin jagorancin Barista Mairiam Haruna Kolo ta shiga tsakani dan bin hakkin yaron da daukar dawainiyar kulawa da lafiyar jaririn da taimakon gwamnatin jihar Neja.

samndaads

Tunda farko kwararrun likitoci na babbar asibitin kwararru na tunawa da Janar Ibrahim Babangida da asibitin kwararru na gwamnatin tarayya, sun yi nasarar yiwa jaririn aikin farko na toshe jijiyoyin da suka samu illa tare da bayyana cewa aiki uku za a yiwa jariri kuma zai warke tare da bada tabbacin za a iya yi mai dashe ta yadda shi ma zai iya anfanar da kanshi wanda ake kyautata zaton zai iya barbarar mace kuma har ta haihu.

Maigirma gwamnan Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello ya taimaka gaya bayan aikin farkon an sake kai shi asibitin kawararru da ke kasar Amurka dan yin aiki na biyu wanda shi ma an samu nasarar yin aikin bisa taimakon gwamnatin jihar Neja.

Dangane da mai lafin kuwa, Barista Mairiam Kolo tace tun da alkali ya wurga ta gidan hursuna da sunan zaman jiran hukuncin kotu har zuwa yanzu ba wani abu da suka ji game da mai laifin. “ A cewarta kamar yadda alkalin ya bayyana mai laifin, za tai zaman jiran hukunci ne har ranar da hukumar da ke bada shawara akan hukunce-hukunce laifuka DPP ta mika rahotonta.Wannan maganar yanzu wajen shekara daya da watanni ke nan ake yin ta.

A cewarta lallai ba zamu yi sanyin kafa ba.sai hukumar ta tabbatar an hukunta mai laifin.“Ban yi nadama ba kuma mun samun gagarumar nasara sosai domin gwamnatin jiha da kungiyoyi masu zaman kansu sun taimaka dan ceto rayuwar yaron. Hukumata ba za tai kasa a guiwa ba sai ta tabbatar an hukunta wannan matar domin masu hali irin nata su dau darasi.

Ba a hana kishi ba ko a addini akwai kishi, amma ba na halaka mutum ba ko cutar da shi, kuma ma wane irin kishi ne wannan na illata rayuwa ko cutar da yaro kankane”?.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ba Mu Amince Da Cin Fuskar Wani a Soshiyal Midiya ba —Jam’iyyar PDP

Next Post

An Kusa Kawo Karshen Barace-barace A kasar Nan —Goni Sheikh Musa

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
16 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
2 days ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post

An Kusa Kawo Karshen Barace-barace A kasar Nan —Goni Sheikh Musa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version