Aminu Mukhtar Dan-Alhaji">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Yawan Karbo Bashin Da Gwamnati Ke Yi Bai Da Amfani Ga Kasar Nan -Farfesa Dadari

by Aminu Mukhtar Dan-Alhaji
January 16, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Farfesa Dadari
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wani Malami a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa Salihu Adamu Dadari ya koka a bisa yadda gwamnatin tarayya ke yawan karbo bashin kudade daga hukumomin da ke bayar da lamuni na kasashen duniya.

Malamin wanda ya bayyana haka a zantawarsa da wakilinmu a garin Saminaka, ya lura tare da nuna damuwarsa cewa galibin lokuta wadansu jami’an gwamnati marasa kishin kasa kan wawure kudaden bayan an karbo bashin.Don haka ne ya ce karbo bashin da gwamnatin tarayyar ke yi bai da wani amfani ga jama’ar kasa.Ya yi bayanin cewa kafin hukumomin bayar da lamunin su bayar da bashin ga kasar nan sai sun gindaya tsauraran sharuda da ka’idoji da sau da yawa kan yi illa ga tattalin arzikin kasa.

samndaads

Farfesa Salihu Dadari ya kawo shawarar cewa a maimakon ci yo bashin, kamata ya yi gwamnatin ta lalubo hanyoyin toshe kafofin da kudadenta ke silalewa, tare da daukar matakan rage tsadar gudanar da harkokin gwamnati.Ya ce cin hanci da rashawa su ne manyan matsalolin da ke targade ci gaban kasar nan da kuma hana ta sakat.

Da ya juya ga batun tsaro kuwa, Malamin jami’ar ya bukaci shugaba Muhammad Buhari ya sallami shugabannin rundunonin tsaron domin kuwa sun gaza kai wa bantensu.Acewarsa, idan aka bai wa mutum mukami kuma ya gaza, ya kamata a sauke shi a kawo wanda ake tunanin zai yi abin da ya dace.Ya nunar da cewa ko harkar tsaron ma tana kara tabarbarewa ne saboda cin hanci da rashawa da suka mata katutu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Korona: Babu Dalilin Da Zai Sa Mu Kafa Dokar Kulle -Fintiri

Next Post

Har Yanzu Ana Sayar Da (DATA) Kan Tsohon Farashi Duk Da Ragin Kashi 50

RelatedPosts

Neja

Tsaro; Sakataren Gwamnatin Neja Ya Nemi ‘Yan Bindiga Su Aje Makamai

by Aminu Mukhtar Dan-Alhaji
5 days ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Sakataren gwamnatin Neja, Ahmed Ibrahim Matane...

Tinubu

Sanata Tinubu Ya Bukaci A Kara Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Al’umma

by Aminu Mukhtar Dan-Alhaji
5 days ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa, Jagoran jam'iyyar babbar jam’iyya mai mulkin...

Miyagun Kwayoyi

Shugaban NDLEA Ya Yi Alkawarin Fattatakar Dillalan Miyagun Kwaya A Nijeriya

by Aminu Mukhtar Dan-Alhaji
5 days ago
0

Daga Bello Hamza, Shugaban hukumar NDLEA, Brig. Gen. Buba Marwa...

Next Post
DATA

Har Yanzu Ana Sayar Da (DATA) Kan Tsohon Farashi Duk Da Ragin Kashi 50

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version