Yawon Bude Ido Na Hutun Ranar ‘Yan Kwadago A Kasar Sin Zai Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawon Bude Ido Na Hutun Ranar ‘Yan Kwadago A Kasar Sin Zai Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

byCMG Hausa
2 years ago

Wasu rahotanni na cewa, tattalin arzikin duniya zai samu tagomashi daga tafiye tafiyen yawon bude ido da Sinawa za su gudanar zuwa kasashen waje, a lokacin hutun ranar ‘yan kwadago ta bana, daya daga cikin lokutan hutu mafiya tsayi a kasar Sin.

A bana Sinawa masu tarin yawa sun shirya ziyartar wurare da dama, a karon farko bayan shafe shekaru 3 ana aiwatar da tsauraran matakan yaki a annobar COVID a cikin kasar, wanda hakan ya haifar da takaituwar tafiye tafiye. Kaza lika bikin na bana, na gudana ne tun daga ranar 29 ga watan Afirilu zuwa 3 ga watan Mayun nan. Shi ne kuma biki mafi tsayi na farko da ake yi a kasar, tun bayan sake bude zirga zirga ta rukunonin masu fita yawon shakatawa daga kasar a watan Fabarairun da ya gabata.

  • Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

A cewar hukumar lura da harkokin yawan shakatawa ta MDD, Sinawa masu yawon bude ido ne ke kan gaba a duniya, wajen bunkasa kasuwar kasa da kasa a fannin, inda yayin tafiye-tafiye da suka gudanar zuwa ketare, tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019, suka kashe kimanin dalar Amurka biliyan 260 a kowace shekara.

Alkaluman shahararren kamfanin samar da hidimomin tafiye tafiye na kasar Sin Ctrip, sun nuna adadin masu duba tikitin jiragen sama a wannan lokaci ya karu da ninki 9, sama da na makamancin lokaci na bara, kuma masu neman hidimomin tafiye-tafiye zuwa ketare sun karu da ninki 18.

Har ila yau, wani rahoto daga kamfanin tantance alkaluma game da harkokin kasuwanni da cinikayya na Euromonitor International, ya nuna cewa, karuwar adadin masu tafiye tafiyen na wannan karo, ya zo a gabar da hada hadar sayayya ke kara fadada a kasar Sin.

Rahoton ya ce bisa matsakaicin hasashe, Sinawa masu fita yawon bude ido na kashe kudaden da suka ninka na shekarar 2019 har sau biyu. Ana hasashen Sinawa masu tafiya yawon shakatawa za su zamo a sahun gaba, a fannin samar da kudaden shiga, ga kantuna marasa dora haraji kan hajojin su, a jimillar fannoni 6 cikin 10 na kasuwanni mafiya muhimmanci, matakin da zai samar da harajin sayayya da darajar sa za ta kai kimanin dalar Amurka biliyan 117. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version