Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

An Yi Kira Ga Shugaba Buhari Da Ya Yi Watsi Da Tayin Sake Tsayawa Takara

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba,  Kaduna

Sakamakon kiraye-kirayen da ake yi wa Shugaba Muhammadu Buhari na ya sake tsayawa takara a zaben kasa ta shekarar 2019, wani Soja mai ritaya, Manjo Mohammed Bashir Shu’aibu Galma, ya shawarci Buharin da ya yi koyi da marigayi tsohon shugaban kasar Afirka ta kudu Nelson Mandela na kin fito wa takarar.

Galma, ya bada shawarar ce a wata ganawa da ya yi da manema labarai a Kaduna.

Ya ce, ganin cewar Shugaba Buhari Dattijo ne, kuma ya taba rike mukamin shugaban kasa a karshin mulkin soja gashi kuma yanzu ya zama shugaban kasa karkashin mulkin farar hula, kin tsayawarsa takara a shekarar 2019 zai  kara masa kima a idon duniya, kamar yadda marigayi Mandela ya yi na kin fito wa takara a kasar shi.

Galma wanda yana daya daga cikin mambobin Cibiyar Buhari ta kasa, ya ci gaba da cewa, Shugaba Buhari kusan duk ya cika alkawuran da ya daukar wa ‘yan Nijeriya lokacin yakin neman zabe, “kamata ya yi ya nuna dattaku ya ki fitowa kamar yadda wasu ‘yan kasa suke ta kiraye-kiraye na ya sake tsayawa takara.

Ya yi misali da cewar, shugaba Buhari ya yi alkawarin samar da tsaro da yakar cin hanci da rashawa da ya zamo rowan dare a kasar nan kuma ya samu cin nasara, ya yi alkawarin dai-daita tattalin arzikin kasa kuma ya cika, inda hakan ya janyo masa yabo har daga kasashen ketare.

Galma, ya kuma shawarci shugaban da ya yi tankade da rairaya a cikin ministocinsa, inda ya ce musamman ministocin da ba su taka wata rawar gani ba wajen gudanar da ayyukan ma’aikatunsu, ko kuma ya rage wa masu nauyin da ya dora musu ta hanyar raba ma’aikatunsu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar Likitoci Ta Janye Yajin Aikin Da Ta Fara

Next Post

Rashin Tabbas Kan Zabukan Kananan Hukumomin Jihar Nasarawa

RelatedPosts

Amin

Yadda Ta Kaya A Taron Tunawa Da Malam Aminu Kano Karo Na 19

by Muhammad
1 day ago
0

Mun Gamsu Da Yadda Aka Tsara Taron Kan Tsaro Da...

AKCOE

Mataimakin Shugaba Kwalejin AKCOE Ya Zama Jakadan Zaman Lafiya A Nijeriya

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Mataimakin Shugaban Kwalijin Ilimi ta Aminu Kano...

Allah

An Roki Al’umma Su Dogara Ga Allah  

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Alhaji Bello Otunba wanda yake daya...

Next Post

Rashin Tabbas Kan Zabukan Kananan Hukumomin Jihar Nasarawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version