Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

An Yi Kira Ga Shugaba Buhari Da Ya Yi Watsi Da Tayin Sake Tsayawa Takara

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba,  Kaduna

Sakamakon kiraye-kirayen da ake yi wa Shugaba Muhammadu Buhari na ya sake tsayawa takara a zaben kasa ta shekarar 2019, wani Soja mai ritaya, Manjo Mohammed Bashir Shu’aibu Galma, ya shawarci Buharin da ya yi koyi da marigayi tsohon shugaban kasar Afirka ta kudu Nelson Mandela na kin fito wa takarar.

samndaads

Galma, ya bada shawarar ce a wata ganawa da ya yi da manema labarai a Kaduna.

Ya ce, ganin cewar Shugaba Buhari Dattijo ne, kuma ya taba rike mukamin shugaban kasa a karshin mulkin soja gashi kuma yanzu ya zama shugaban kasa karkashin mulkin farar hula, kin tsayawarsa takara a shekarar 2019 zai  kara masa kima a idon duniya, kamar yadda marigayi Mandela ya yi na kin fito wa takara a kasar shi.

Ya yi misali da cewar, shugaba Buhari ya yi alkawarin samar da tsaro da yakar cin hanci da rashawa da ya zamo rowan dare a kasar nan kuma ya samu cin nasara, ya yi alkawarin dai-daita tattalin arzikin kasa kuma ya cika, inda hakan ya janyo masa yabo har daga kasashen ketare.

Galma, ya kuma shawarci shugaban da ya yi tankade da rairaya a cikin ministocinsa, inda ya ce musamman ministocin da ba su taka wata rawar gani ba wajen gudanar da ayyukan ma’aikatunsu, ko kuma ya rage wa masu nauyin da ya dora musu ta hanyar raba ma’aikatunsu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar Likitoci Ta Janye Yajin Aikin Da Ta Fara

Next Post

Rashin Tabbas Kan Zabukan Kananan Hukumomin Jihar Nasarawa

RelatedPosts

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Kasuwar Mile 12

Kwamitin Da Shugaban Kasuwar Mile 12 Ya Nada Na Cigaba Da Jajanta Wa Manoman Arewacin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Sabon kwamitin da Babban Shugaban kasuwar mile 12 Intanashinal market...

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

Next Post

Rashin Tabbas Kan Zabukan Kananan Hukumomin Jihar Nasarawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version