Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

An Yi Wa Ɗan Shekaru 70 Rajamu Har Lahira A Kano

by Tayo Adelaja
October 11, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Musa Ahmad, Kano

A jiya ne wani babban alƙalin majistire ta Birnin Kano, ya tasa ƙeyar wasu mutum biyar zuwa gidan yari kafin a ci gaba da sauraron shari’arsu, waɗanda ake zargi da laifin garkuwa tare da jefe wani tsoho ɗan shekaru 70 mai suna Usman Ɗanbuba.

Waɗanda ake zargin sune;  Wada Mohammed ɗan shekaru 30, Ya’u Muhammad ɗan shekaru 22, Musa Inusa ɗan shekaru 35, Sale Buba ɗan shekaru 27 da kuma Sule Garba ɗan shekaru 45.

Kotun ta zarge su da laifuka waɗanda suka haɗa da; shirya ɓarna, garkuwa, fashi da makami, kisa da kuma mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

Ɗan sandan da ya shigar da ƙara, waɗanda ake zargin sun yi garkuwa da mamacin ne, inda suka yi masa fashin naira 85,000 da babur ɗinsa. “Bayan sun yi garkuwa da shi, sai waɗanda ake zargin suka ɗauke shi zuwa Tsaunin Shetu da ke dajin Falgore na jihar Kano, sannan suka nemi da a kawo kuɗin fansa naira miliyan biyar.” Inji ɗan sandan

Ya ƙara da cewa, lokacin da iyalan mamacin suka gaza haɗa wannan kuɗin, sai waɗanda ake zargin suka yi wa Ɗanbuba rajamu har lahira a ranar 22 ga watan Mayu.

Ɗan sanda mai ƙara ya zayyana cewa, waɗanda suke zargin sun aikata babban laifi wanda ya saɓa dokar sashe na 97, 17, 15 na dokokin ta’addanci, fashi da makami da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba. Sai dai ya zuwa haɗa wannan rahoton, waɗanda ake zargin sun ƙi amsa laifinsu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Abin Kunya A Kaduna: Malamai 21,780 Suka Faɗi Jarabawar ‘Yan Firamare

Next Post

Barin Takarar 2019 A Arewa: Ƙusoshin PDP Sun Yi Wa Abuja Ƙawanya

RelatedPosts

Hijira

Zulum Ya Bankado ’Yan Hijira 650 Na Bogi

by Muhammad
11 hours ago
0

Ya Sake Koma Wa Dikwa Bayan Harin Boko Haram Daga...

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
2 days ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Next Post

Barin Takarar 2019 A Arewa: Ƙusoshin PDP Sun Yi Wa Abuja Ƙawanya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version