Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2019: PDP Ta Gargaɗi ‘Ya’yanta Su Kiyaye Dokar INEC

by
5 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga El-Mansur Abubakar, Gombe

Ƙungiyar ci gaban Haruna Garba dake kiran Ambasada Haruna Garba Magayaƙin Gombe da ya amsa kiransu ya fito takarar kujerar gwamnan jihar Gombe a zaɓen shekarar  2019 ta Haruna Garba Solidarity group a karkashin tutar jam’iyyar PDP ta gargaɗi mambobinta da su kiyaye dokokin INEC.

Wannan gargaɗi da ƙungiyar tayi yana dauke ne a wata takarda da suka aikewa yan jarida ranar Laraba a Gombe mai dauke da sanya hannun Alhaji Yari Na Alhaji Gambo Isari.

Labarai Masu Nasaba

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Alfanun Koyon Harsunan Kasashe Ga Daliban Kimiyya – Farfesa Gwarzo

Da suke yabawa hukumar zaɓen ta kasa INEC kan jadawali da lokutan zaɓe da hukumar ta fitar na zaɓen shekara ta 2019 sun lura hukumar zaɓen ta Ja kunnen jam’iyyun siyasa da yan takara na kaucewa fara gudanar a tarukan siyasa da yaƙin neman zaɓe tunda lokaci bai yi ba.

Har Ila ƙungiyar ta Haruna Garba solidarity group ta sake gargaɗin mambobinta da magoya bayan Sanata Haruna Garba da su gujewa ayyukan da suka saɓawa tsarin dokokin hukumar zaɓen ta INEC dan gudun samun matsala.

Ƙungiyar ta yi amfani da wannan damar ta shaidawa duniya cewa su masu biyayya ne ga tsarin doka sannan kuma za su kiyaye gudanar da ayyukan da suka saɓawa dokar kasa da ta hukumar zaɓen ta INEC.

“ Babu wani ko wata da yake ikirarin nuna goyon bayansa ga Sanata Haruna Garba da zai yi amfani da sunan wannan ƙungiyar ya karya dokar hukumar zaɓe ta INEC “ A cewar ƙungiyar.

Daga nan sai Alhaji Yaro Na Alhaji Gombo Isari, a ƙungiyance yace suna nemi hadin kan yan jarida a fadin jihar Gombe wajen taimakawa suna yayata aikace- aikacen ƙungiyar dan a san abubuwan da suke gudanarwa.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar zaɓen ta INEC a kwanakin baya ne  ta fitar da tsarin jadawali da ranakun zaɓuɓɓukan dake tafe na shekarar ta 2019 inda za’a gudanar da zaɓen shugaban kasa dana yan majalisun Tarayya a ranar 16 ga watan Fabarairu.

Zaɓen gwamnoni da yan majalisun jihohi zai gudana a ranar 2 ga watan Maris kuma dukkan yaƙin neman zaɓe an hana har sai saura kwanakin 90 Kafin ranar zaɓe.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Wajibinmu Ne Daƙile Sake Ɓarkewar Yaƙin Basasa –Buhari

Next Post

Lamarin ‘Yan Siyasa Na Da Ban Tsoro –Matasan Arewa

Labarai Masu Nasaba

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
1 day ago
0

...

Alfanun Koyon Harsunan Kasashe Ga Daliban Kimiyya – Farfesa Gwarzo

Alfanun Koyon Harsunan Kasashe Ga Daliban Kimiyya – Farfesa Gwarzo

by Khalid Idris Doya
1 day ago
0

...

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

by
2 days ago
0

...

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

by
3 days ago
0

...

Next Post

Lamarin ‘Yan Siyasa Na Da Ban Tsoro –Matasan Arewa

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: