Sagir Abubakar">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Za A Bai Wa Daliban Da Suka Gama Jami’a Da Maki Mafi Tsoka Aiki A Katsina

by Sagir Abubakar
December 4, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Jami’a
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan Jihar Katsina Aminu Bello Masari ya amince da daukar daliban jami’ar UMY aikin gwamnati wadanda suka gama karatu da maki mafi girma a matakin digiri na daya (first class). Ya ce hakan nada nufin tabbatar da ganin matasa maza da mata masu hazaka sun shiga cikin aikin gwamnati don a samu ci gaba.

Gwamnan ya bayyana cewar a wajen taron nuna hazaka a Jihar Katsina na kasa mai nufin zakulo hazikan matasa da ya gudana a hedkwatar daukar ma’aikatan kananan hukumomi ta Jihar.

samndaads

Ya ce gwamnatin shi ta ba bangaren ilimi fifiko don tabbatar da cigaba. Kamar yadda yace bullo da jarabawar kwalfayin da gwamnatinshi tayi ya haifar da da mai ido. Ya yi nuni da cewa a shekarar (2019) Jihar Katsina ta zama zakara a gasar muhawara ta shugaban kasa ya kuma kara da cewa yanzu haka Jihar na cikin gasar ta wannan shekara.

Gwamnan ya kuma yabama wadanda suka shiga gasar zakulo hazakan sai ya yi fatan cewa za a yi adalci wajen zaben wanda ya fi daga cikin wadanda suka fito cikin gasar.

A wani labari makamancin wannan majalissar dokokin Jihar Katsina ta zartas da dokar shekarun aje aiki ga malaman da ke shiga aji da wadanda basu shiga aji na kwalejin kimiyya ta Hassan Usman Katsina daga shekaru (65) ko kuma shekaru (40) ana aiki.

Majalissar zartaswar ta mika kudurin dokar ga majalissar domin a yi mata garanbawul domin ta samar da shekaru (40) ana aiki ko kuma cimma shekaru (65) da haihuwa ga ma’aikatan da basu shiga aji na kwalejin.

Matakin ya biyo bayan nazarin rahoton kwamitin kula da lamurran ilimi mai zurfi. Jagoran majalissar Abubakar Suleiman Abukur ya gabatar da kudurin dokar aka yi mata karatu na (3).

Mataimakin shugaban majalissar injiniya Shehu Dalhatu tafoki wanda ya jagoranci zaman majalissar na wannan Larabar ya bayyana cewa zartas da dokar na daya daga cikin nasarorin da gwamnatin APC ta samu a jihar dama majalissar dokoki mai ci yanzu.

Injiniya Shehu tafofi ya ce ma’aikatan da basu shiga aji na manyan makarantun gaba da sakandire a jihar nan, na daga cikin masu ruwa da tsaki wajen tafiyar da sha’anin mulki na irin wadannan makarantu.

Tun da farko, shugaban kwamitin Shamsuddeen Abubakar Dabai wanda ya gabatar da rahoton ya roki majalissar da ta amince da dukkanin garanbawul din da aka yima dokar ta 2017.

SendShareTweetShare
Previous Post

Mu’ujizozin Annabi Muhammadu (SAW); Karatu Na Bakwai

Next Post

Karshen Tika-tika-tik: Maina Ya Shiga Hannu

RelatedPosts

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Sagir Abubakar
3 mins ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

DATA

Har Yanzu Ana Sayar Da (DATA) Kan Tsohon Farashi Duk Da Ragin Kashi 50

by Sagir Abubakar
24 hours ago
0

Yawancin masu amfani da layin sadarwa sun ce har yanzu...

Farfesa Dadari

Yawan Karbo Bashin Da Gwamnati Ke Yi Bai Da Amfani Ga Kasar Nan -Farfesa Dadari

by Sagir Abubakar
24 hours ago
0

Wani Malami a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa...

Next Post
Maina Ya Shiga Hannu

Karshen Tika-tika-tik: Maina Ya Shiga Hannu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version