Umar A Hunkuyi">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Za A Dauki Nakasassu Sama Da Dubu Aikin Gwamnati A Kwara

by Umar A Hunkuyi
July 31, 2020
in LABARAI
1 min read
Za A Dauki Nakasassu Sama Da Dubu Aikin Gwamnati A Kwara
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Nakasassu Dubu daya Da dari Shida ne za su amfana da shirin bai wa matasa ayyukan yi na watanni uku na gwamnatin tarayya a Jihar Kwara.
Shugaban kwamitin shirin a Jihar, Oluwasegun Oyewo, ne ya bayyana hakan a bayan da ya yi wata ganawa da hadaddiyar kungiyar shugabannin masu nakasa a Jihar, in da ya ce wannan adadin yana daidai ne da kashi 10 na mutanan da za su amfana su 16,000 a shirin cikin Jihar.
Ya kara da cewa, mutane 1,000 ne za a dauka daga kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomin Jihar 16. Wadanda kuma za a dauka din tilas ne su kasance a tsakanin ‘yan shekaru 18 zuwa shekaru 50, sannan tilas ne kashi 20 daga cikinsu su kasance masu ilimi ne, hakanan kaso 30 a cikinsu lallai su kasance mata ne.
Oyewo ya ce ba lallai ne wadanda za a daukan su kasance ‘yan asalin karamar hukumar ba, amma tilas ne su kasance mazauna karamar hukumar ce. Ya kara da cewa, ba kuma lallai ne wadanda za a daukan su kasance sun iya wata sana’a ba.
A cewar sa, za a fara gudanar da shirin ne daga watan Oktoba zuwa watan Disamba, 2020, za kuma a rika bai wa wadanda suke a cikin shirin tallafin naira 20,000 a kowane wata.
Sarkin Ilori, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, wanda Malam Salihu Balogun ya wakilce shi, ya yaba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, a kan samar da ayyukan yi ga matasa 774,000 a cikin shirin, wanda ya kwatanta da cewa abin a yaba ne.

SendShareTweetShare
Previous Post

Zulum Ya Kalubalanci Sojoji A Kan Harin Da Boko Haram Ta Kai Masa

Next Post

Duk Dalibin Da Ke Shaye-Shaye Ba Zai Sami Gurbin Karatu A Jihar Kaduna Ba – Dakta Maigari

RelatedPosts

"yan fashi

Annobar Sace Farfesoshi Ta Kunno Kai A Arewa

by Umar A Hunkuyi
5 hours ago
0

An Sace Farfesa, An Kashe Dansa Da Mutum Uku A...

Kwamishinan Labarai

Korona: Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Taruka, Ta Umarci Ma’aikata Su Yi Zaman Gida

by Umar A Hunkuyi
5 hours ago
0

Gwamnatin Jihar Kano ta bada umarnin sake kafa dokar rufe...

Kwamishinan Labarai

Korona: Gwamnatin Ganduje Ba Ta Son Garkame Kano – Kwamishinan Labarai

by Umar A Hunkuyi
5 hours ago
0

Gwamnatin Jihar Kano a karkashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje...

Next Post
Duk Dalibin Da Ke Shaye-Shaye Ba Zai Sami Gurbin Karatu A Jihar Kaduna Ba – Dakta Maigari

Duk Dalibin Da Ke Shaye-Shaye Ba Zai Sami Gurbin Karatu A Jihar Kaduna Ba – Dakta Maigari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version