Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila
  • English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Ministoci

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, ya ce da yiyuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta kirkiro wasu sabbin ma’aikatu da za su zama kari kan wadanda ake da su. 

Femi ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis a Abuja, inda ya ce bayan jerin ministoci 28 da Tinubu ya gabatar, zai kuma sake aikewa da sunayen mutum 13 nan gaba kadan.

  • Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes
  • Gwamman Zamfara Ya Karrrama Hajiyar Da Ta Tsinci Dala 80,000 A Saudiyya

Ya ce, ministocin da aka gabatar sai da suka tsallake tantancewar shugaban kasa da kansa.

Ya ce ba ya ga sunan mutum 28 da Tinubu ya gabatar a matsayin ministoci, zai kuma sake aikewa da kashi na biyu na ministocin da suka kunshi sunayen mutum 13.

“Kamar yadda kuka sani kwanaki 60 da rantsuwa, kamar yadda yake kunshe cikin kundin tsarin mulki. Ya cika ka’idar ya gindaya ta hanyar tura sunayen mutum 28 a yau.

“Kamar yadda aka karanta cikin wasikarsa a gaban majalisar dattawa, akwai karin sunayen da za a gabatar, babu tabbacin su nawa ne amma wakila za su haura 12, za a tura sunayen ga majalisar dattawa nan da ‘yan kwanaki.”

Kamfanin Dillacin Labarai (NAN) ta ruwaito cewa Gbajabiamila ne ya gabatar da jerin sunayen ministocin da Tinubu ya zaba kuma shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta a majalisar.

Ministocin da aka zaba 28 su ne: Abubakar Momoh, Yusuf Maitama Tuggar, Ahmed Dangiwa, Hannatu Musawa, Chif Uche Nnaji, Dokta Betta Edu, Dokta Doris Aniche Uzoka, David Umahi da Nyesom Wike.

Sauran su ne Badaru Abubakar, Nasiru Ahmed El-Rufai, Ekperipe Ekpo, Nkeiruka Onyejocha, Olubunmi Tunji Ojo, Stella Okotette, Uju Kennedy Ohaneye, Mista Bello Muhammad Goronyo, Mista Dele Alake, da Mista Lateef Fagbemi.

Akwai kuma Mista Muhammad Idris, Mista Olawale Edun, Mista Waheed Adebayo Adelabu, Misis Iman Suleiman Ibrahim, Farfesa Ali Pate, Farfesa Joseph Utsev, Sanata Abubakar Kyari, Sanata John Enoh, da kuma Sanata Sani Abubakar Danladi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Next Post
Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version