Za A Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tsaro Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tsaro Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

byCGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Da yammacin yau Alhamis ne aka gudanar da taron manema labarai, a ma’aikatar tsaron kasar Sin, inda kakakin ma’aikatar kanar Zhang Xiaogang, ya ce a shekarun baya bayan nan, alakar harkokin soji tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka na kara zurfafa. Kaza lika sassan biyu, sun gudanar da dandalin zaman lafiya da tsaro, da taron musamman kan hakan, suna kuma ci gaba da yin musaya ta kut da kut a dukkanin matakai.

Zhang, ya kara da cewa, Sin da kasashen Afirka sun ci moriyar hadin gwiwa a sassa kamar na gina tsarin aikin soji, da horas da dakaru, da tsaron teku, da ayyukan wanzar da zaman lafiya, da bunkasa kiwon lafiya, da ayyukan ceton jin kai da na dakile bala’u.

  • GDPn Kasar Sin Na Shekarar 2023 Ya Karu Da Kashi 5.2 Cikin Dari
  • Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

Jami’in ya ce rundunar sojin Sin za ta ci gaba da daukaka akidun gaskiya,

da cimma sakamako na zahiri, da tabbatar da tafiya tare, da amincewa juna, da aiki tare da sauran rundunonin sojin kasashen Afirka, wajen ingiza aiwatar da muhimman manufofi da jagororin su suka cimma matsaya a kai. Har ila yau, sassan biyu za su karfafa tuntubar juna bisa matsayin koli, da hadin gwiwa na zahiri.

A daya hannun za su kara inganta hadin gwiwa mai ma’ana da karko, da samar da tabbacin aminci na tsaro, ta yadda za a gina al’umma mai makomar bai daya bisa matsayin koli tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da bayar da babbar gudummawa ta wanzar da tsaron yankuna da duniya baki daya, da yayata gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil Adama.

Don gane da aiwatar da tsarin rakiyar jiragen ruwa, da rundunar sojin ruwan Sin ke gudanarwa a tekun Aden da yankunan ruwan Somalia kuwa, Zhang Xiaogang ya ce wannan batu ne wanda ba shi da wata nasaba da halin da ake ciki yanzu haka a yankin. Don haka Sin za ta ci gaba da aiwatar da manufofin tsaron kasa da kasa, da tabbatar da kariya a hanyoyin tekunan kasa da kasa, da samar da tsarin sufurin teku abun dogaro, wanda zai ci gaba da rake jiragen ruwan Sin da ma na sauran kasashe. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version