Za A Yi Gaggarumin Taron Bunkasa Noma A Legas
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Yi Gaggarumin Taron Bunkasa Noma A Legas

•Obasanjo Da Masana Aikin Gona Za Su Halarta

byAbubakar Abba
1 year ago
Aikin Gona

Tsohon Shugaban Kasar Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo da sauran wasu masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, za su halarci wani gagarumin taro a kan aikin noma da ake kira a turance ‘AgriConnect a 2024’.

Za a shirya wannan taro ne, don tattaunawa a kan yadda za a lalubo mafita wajen bunkasa fannin aikin noma a Nijeriya.

  • Yadda Sha’anin Noman Abarba Ke Taimakawa Kyautata Zaman Rayuwar Mazauna Wasu Kauyuka A Kasar Sin
  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

Kazalika, taron wanda za a gudanar a ranar 31 ga watan Mayun 2024, zai taimaka wajen hadaka tare da yin amfani da fasahar kere-kere, musamman don magance kalubalen da fannin aikin noma na wannan kasa ke fuskanta.

Har ila yau, taken taron shi ne, ‘Cike gibi ta hanyar yin hadaka tare da amfani da kirkire-kirkiren fasahar zamani, domin sama wa fannin aikin noma alkibla mai dorewa a nan gaba a fadin wannan kasa’.

Bugu da kari, taron na kwana guda, za a gudanar da shi ne a dakin taro na Cibiyar Landmarl event da ke Jihar Legas.

Kazalika, taron zai samu halartar masu ruwa da tsaki daga fannin kimiyya, ‘yan kasuwa a fannin aikin noma, cibiyoyin hada-hadar kudi da za su bayar da gudanunwarsu ga kanana da kuma manyan masu noma, domin samun riba da kuma yadda manoman za su rungumi wannan aiki na noma ta hanyar yin amfani da fasahar zamani tare da kuma ilimantar da su dabarun yin noma na zamani.

Mashiryin taron, Dakta Toyosi Obasanjo; a wata sanarwa da ya bai wa LEADERSHIP ya tabbatar da cewa, taron zai yi matukar taimakawa wajen cike gibin da ake da shi a wannan fanni na aikin noma da kuma kara karfafa hadaka da masu ruwa da tsaki daban-daban.

A cewarsa, daya daga cikin manufar taron ita ce, samar da dabarun da za su taimaka wajen magance kalubalen da fannin aikin noma na wannan kasa ke fuskanta tare kuma da samar da wadataccen abinci a fadin kasar baki-daya.

Ya sanar da cewa, Tsohon Shugaban Kasa; Cif Olusegun Obasanjo ne zai kasance shugaban wannan taro, wanda kuma sauran wadanda aka gayyata wadanda suka hada da mahukunta daga Bankin Masana’antu na Kasa, Bankin Union, Jakadan Faransa, USAID, IITA da kuma Microsoft, za su gabatar da kasidu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Yadda Sarki Sunusi Lamido Ya Yi Bikin Shiga Fadar Kano Tsakar Dare

Yadda Sarki Sunusi Lamido Ya Yi Bikin Shiga Fadar Kano Tsakar Dare

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version