Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Za Mu Ƙarfafa Ƙungiyoyin Matasa Na Cigaba – Shugaban ALGON Na Abuja

by Tayo Adelaja
October 6, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi, reshen Babban Birnin Tarayya Abuja (ALGON), Hon. Joseph Shazin Kwau ya bayyana aniyasu ta ba da goyon baya ga ƙungiyoyin da ke tallafa wa cigaban matasa ta kowace fuska.

Shugaban ƙungiyar wanda har ila yau shi ne Shugaban Ƙaramar Hukumar Kwali, ya bayyana haka a sa’ilin da ake bikin ƙaddamar da Ƙungiyar Matasa Masu Shan Shayi (Shayi Youth Association) a Gwagwalada.

samndaads

Wanda mai taimaka masa na musamman a kan yaɗa labarai, Alhaji Iya Pai ya wakilta, shugaban na ALGON ya bayyana cewa kasancewar matasa ƙashin bayan cigaban al’umma suna buƙatar a ƙarfafa musu gwiwa kan aikace-aikacensu da za su kawo haɓakar tattalin arziƙi da kwanciyar hankali a tsakanin jama’a.

“Kamar yadda kuka sani, shi Shugaban Ƙaramar Hukumar Kwali tsohon malamin makaranta ne, ya yi ciyaman a baya, a yanzu kuma aka sake dawo da shi saboda ƙwazonsa. Shi mutum ne mai ba da goyon baya ga ƙungiyoyi domin su iya dogaro da kansu. Kamar yanzu a Kwali akwai ƙungiyoyi da yawa da yake taimaka masu da wasu abubuwa da za su ƙarfafa su”.

“Idan matasa suna da abin yi ba za a samu aikata munanan laifuka ba, za ka ga sun mayar da hankali kan abin da zai amfane su. Rashin sana’a yake kawo duk abubuwan da ba su dace ba a wurin matasanmu. Shi ya sa saboda muhimmancin wannan taron ya shirya da kansa zai zo sai kuma wani uzuri ya faɗo. Amma ya umurce ni in koma in shaida masa duk abin da ya gudana a wannan taron kuma zan isar masa da yardar Allah”. In ji shi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Mai Ɗaukan Hoto Na Jarida Hannu Biyu Yake Aiki — Abdullahi

Next Post

Munazzamatu Fityanul Islam Ta Buɗe Reshe A Suleja

RelatedPosts

Dan Majalisar Tarayya Ya Sabunta Katin Jam’iyyar APC A Funtuwa

Dan Majalisar Tarayya Ya Sabunta Katin Jam’iyyar APC A Funtuwa

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Funtua  Dan majalisar Tarayya me wakiltar mazabar...

Sace Daliban Zamfara: Sarkin Musulmi Da Gwamna Tambuwal Sun Kai Ziyarar Jaje

Sace Daliban Zamfara: Sarkin Musulmi Da Gwamna Tambuwal Sun Kai Ziyarar Jaje

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, kasa da awa goma sha biyu da...

miyagun kwayoyi

Masu Garkuwa Da Mutane Muggan Kwayoyi Suke Bukata Matsayin Kudin Fansa – NDLEA

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa Shugaba kuma babban jami’i na Hukumar...

Next Post

Munazzamatu Fityanul Islam Ta Buɗe Reshe A Suleja

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version