Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3

Gina Sabon Titi Ne Ya Dace Da Hanyar -  Gwamna Bala

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Hanyar Bauchi

Kamfanin da gwamnatin tarayya ta bai wa aikin kula da kwaskwarima na babban hanyar Bauchi zuwa Gombe, Anaco Nigeria Limited, ya sha alwashin gyara hanyar da ta yanke a daidai gadar Kaljanga cikin kwanaki uku masu zuwa. 

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, a sakamakon mamakon ruwan sama da aka tafka a safiyar ranar Lahadi wanda ya yi sanadin ruftawar gadar, lamarin da janyo raba jihohin da ke yankin arewa maso gabas daga zuwa sauran yankunan kasar nan.

  • Matafiya Sun Makale Sakamakon Ruftawar Gada A Hanyar Gombe Zuwa Bauchi

Lamarin ya tilasta wa wasu matafiyan fasa tafiyar yayin da wasu kuma suka yi zagaye mai nisa domin samun damar zuwa wuraren da suke son zuwa.

Kodayake, kamfanin ya ce nan da kwanaki uku za su yi garanbawul ga hanyar ta yadda motoci za su samu damar wucewa.

Wakilinmu ya labarto cewa ba wannan ne karo na farko da hanyar Bauchi zuwa Gombe ke yankewa ba, sai dai ba a taba samun yankewar hanyar ba kamar na wannan lokacin.

Gwamna Bala Muhammad da ya ke maida jawabi jim kadan bayan wakilin kamfanin kwangilar ya bada tabbacin kammala kwaskwarimar cikin Kwana Uku, ya ce, wannan lamarin ya janyo kunci ga jama’a kuma zai shafi tattalin arzikin jama’a muddin ba a yi gaggawar daukar matakin gyara hanyar cikin kankanin lokaci ba.

Bala ya ce, hanyar ta gaji ne gaba daya ba ta bukatar wata kwaskiwarima, sake ginawa ne ya dace da ita.

Ya bukaci gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da ta duba halin da hanyar ke ciki domin sake bayar da kwangilar sake ginawa, ya nuna takaicinsa kan yadda gwamnatin baya ta Muhammadu Buhari ta yi watsi da hanyar duk da tsananin bukatar agajin gaggawa da hanyar ke bukata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Neymar Jr Ya Koma Kungiyar Al Hilal Ta Kasar Saudiya Da Taka Leda

Neymar Jr Ya Koma Kungiyar Al Hilal Ta Kasar Saudiya Da Taka Leda

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version