Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar

byKhalid Idris Doya
1 year ago
Hasken Rana

Injiniya Abubakar Ibrahim Musa matashi ne a Jihar Bauchi da ke arewacin Nijeriya, wanda ya kware wajen hada Sola Panels, wato faranti mai amfani da haske rana ya mayar da shi zuwa lantarki da sauran abubuwan kere-kere, ya shaida cewar ta hanyar kera Farantin nan za a iya samar wa dubban ‘yan Nijeriya ayyukan yi.

Abubakar wanda ke da mallakin kamfanin Kuantun Engineering DPS da ke Jihar Bauchi sun kware a bangaren kere-keren abubuwan da suka shafi na solar Panels da sauran abubuwan da ake sarrafa su domin bayar da wutar lantarki daga hasken rana.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan $1.5 Sakamakon Yin Bahaya A Fili

Injiniya Abubakar Ibrahim Musa da aka haifa a 1982 ya shaida cewar ya karanci ilimin fasaha a bangaren injiniyanci na hada kayan wuta wanda ya samu shaidar matakin karatun digiri na biyu yanzu na neman ya uku.

A binciken da wakilinmu ya gudanar kamfanin na kuma horas da matasa da dama kan harkokin da suka shafi injiniyanci na electrical engineering.

Kamfanin ya kware wajen hada Light Bulbs, Solar Panels, Solar Streetlights, Floodlight, Solar Generators da dai sauransu.

Matashin ya ce yana yin kwayayen lantarki da sauran abubuwan da suka shafi lantarki. Ya ce ya hada gwiwwa da wani kawunsa don kirkirar wannnan kamfanin samar da lantarki don tallafa wa al’umma da samar da ayyukan yi ga matasa.

Injiniya Abubakar ya ce wasu kayyakin aikin da suke amfani da su sukan sayo ne daga kasar China, yayin da wasun kuma a Nijeriyar suke samunsu.

Ya ce a kowace rana suna kirkirar solar Panels akalla 60. Ya ce babban kalubalen da yake fuskanta a yanzu shi ne rashin karfin jarin da zai bunkasa kasuwancinsa.

Abubakar ya bayyana cewar sun kirkiri kamfannsu ne lura da yanayin kukan matsin tattalin arziki da ake ciki a kasar nan da kuma rashin aikin yi a tsakanin jama’a.

Ya ce kamfanin nasu suna sarrafa abubuwa da yawa kamar su farantin wuta mai amfani da hasken rana ya maida shi zuwa wutar lantarki (Solar Panel), da kuma yin koyayen hasken wuta na zamani da turakun solar na kan layuka da wasu abubuwa na fasaha.

“Abubuwan da muke sarrafawa kamar shi faranti mai maida hasken rana zuwa wutar lantarki muna samun wasu kayan aikin da muke hadawa wasu kuma saimub shigo da su daga kasar China. Kamar abin da ya shafi Solar Cells da solar ribbon, wires su muna zuwa da sune daga kasar China. Amma irin su

Aluminium profile, glass da sauransu duk muna samu a nan Nijeriya.”

Ya tabbatar da cewar jama’a suna sayen kayansu amma suna bukatar manyan masu sayen da su karfafa musu guiwa wajen sayen abubuwan da suke sarrafawa.

Daga bisani ya yi korafin rashin jari, yana mai cewa harkar da suka shafi Solar suna nan birgik muddin aka dafa lallai za a samu guraben ayyukan yi ga dubban jama’a a Nijeriya da dama da rage dogaro da wutar lantarki a fannoni daban daban.

“Babban burin mu shi ne samar da ayyukan yi a tabbatar ayyuka sun samu a cikin kasa kuma an saukaka wa al’umma.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

Majalisar Wakilan Jama'ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version