Muhammad Maitela">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Zabarmari: Dalilin Da Ya Sa Boko Haram Ke Kashe Jama’ar Borno – Zulum

by Muhammad Maitela
December 3, 2020
in LABARAI
2 min read
Zulum
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya bayyana cewa mayakan Boko Haram suna kashe jama’ar jihar a duk lokacin da suka nuna wa sojojin Nijeriya inda suke.

Gwamnan ya yi wannan furucin ne ta hanyar kakakin sa, Malam Isa Gusau, martani dangane da zarge-zargen da wasu ke yi cewa sojoji ba su samun hadin kan jama’ar jihar wajen ba su cikakken bayanan sirri kan mayakan Boko Haram.

samndaads

A wani bayanin da ya tura a shafin sa na ‘Tweeter’, Isa Gusau ya yi nuni da yadda Boko Haram suka bayar da dalilin da yasa suka kashe manoma a Zabarmari saboda bayanan sirrin su da mutanen garin ke bai wa sojoji.

“Wannan daya ne daga cikin sakamakon da ke biyo bayan hadin kan jama’ar jihar Borno ke bai wa jami’an tsaro tsawon lokaci. Mutane da dama ne suka rasa rayukan su, a duk lokacin da suka tsegunta wa sojoji bayanan sirrin mayakan, kuma har yanzu ba su dena ba. Kuma wasu da dama su kan yi kokarin taimakon sojoji zuwa fagen fama kuma a kashe, kuma duk da hakan basu bari ba. Yanzu kuma sai mu kara jin wani maras ta ido ya bude baki ya zargi jama’ar Borno.”

A ranar Asabar da ta gabata Boko Haram su ka yi wa manoman shinkafa da dama kisan gilla a kauyen Zabarmari, da ke karamar hukumar Jere a jihar.

Da ya ke daukar nauyin wannan aika-aikar kisan gillar, kwamandan mayakan, Abubakar Shekau ya ce sun aiwatar da kai harin ga manoman sakamakon yadda suka kama daya mamban su tare da mika shi ga sojojin Nijeriya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tsaro Da Tattalin Arziki: Buhari Na Cikin Tsaka-mai-wuya

Next Post

’Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda A Kuros Ribas

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Muhammad Maitela
14 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Muhammad Maitela
15 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Muhammad Maitela
19 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post
Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda

’Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda A Kuros Ribas

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version