Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Zaben 2019: Gwamnoni Da Ministoci Na Goyon Bayan Buhari Ya Zarce —Gwamna El-rufai

by Tayo Adelaja
September 10, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba, Kaduna

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i ya bayyana cewa, Shugaban kasa Muhammadu Buhari yana da goyon bayan mafi yawancin gwamnonin jam’iyyar  (APC) da kuma ministoci kan ya sake tsayawa takara a zaben shekarar 2019.

El-Rufai ya bayyana hakan ne ga manema labarai a fadar shugaban kasa jim kaban da kammala ganawar da ya yi da shugaba Buhari a fadar ta shugaban kasa.

Ya ce, “in dai akan takarar shugaba Buhari ce a shekarar  2019, a nawa ra’ayin, shugaban ya samu cikakkiyar lafiyar da zai iya kara tsayawa takarar, kuma burina da addu’a sune ya tsaya takarar.”

Sai dai gwamnan ya karyata labaran kanzon kuregen da ake yadawa akanshi da ke cewa ana renonsa ne don ya gaji shugaba Buhari a kakar zaben shekarar 2019.

Gwamna Nasiru El-rufa’i ya cigaba da cewa, “A matsayina na dan gani kashenin shugaba Buhari. Bani da wani burin neman kujerar shugaban basa kamar yadda ake ta yamibibi dani akan hakan, tun lokacin da nake rike da mukamin ministan Abuja da kuma bayan na bar aiki na Ministan a shekarar 2017 ake ta irin wannan yamibibin.”

Gwamnan ya ce, “Abin da nake son in sanar da duniya shi ne, ban taba zama dan takarar shugaban basa ba, haka nan ban taba zama dan takarar gwamna ba. Na zama gwamna ne a bisa ikon Allah kuma don shugaba Buhari ya ce in fita in tsaya takarar.”

Da aka nemi jin ra’ayinsa akan furucin kwanan baya da ministan mata da walwalar jama’a Aisha Alhasan tayi na cewa ba za ta goyi bayan Shugaba Buhari a zaben 2019 ba, idan har ya tsaya takara. El-Rufa’i ya ce, furucin nata ba wani abin mamaki bane.

Ya ce, “ Ban yi mamakin hakan ba, domin a matsayinta ‘yar Najeriya kuma mutum, tana da damar ta fadi albarkacin bakinta sannan ta kuma goyi bayan wanda take so.”

SendShareTweetShare
Previous Post

LEADERSHIP A YAU: Gabatar Da Jaridar Hausa Ta Farko Mai Fitowa Kullum A Nijeriya

Next Post

Ta Hallaka Dan Kishiyarta Da Maganin Kashe Kwari

RelatedPosts

Jam’iyyar APC Ta Raba Tallafin Kayan Azumi Na Sama Da Naira Biliyan Daya A Zamfara

by Daurawa Daurawa
1 hour ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara, karkashin...

Taho-mu-gama Kan Shugabancin PDP A Kano

Taho-mu-gama Kan Shugabancin PDP A Kano

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Yusuf Shu’aibu   Abin Da Ya Sa Tambuwal Yake...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yadda Za A Kawo Karshen Ta’addanci A Arewa Maso Yamma — Gwamna Ganduje

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhamad Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje...

Next Post

Ta Hallaka Dan Kishiyarta Da Maganin Kashe Kwari

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version