Zaben Fidda-Gwanin APC: A. A Jinjiri Ya Maka Bashir Machina Kotu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fidda-Gwanin APC: A. A Jinjiri Ya Maka Bashir Machina Kotu

byMuhammad Maitela
3 years ago
Machina

Ga dukan alamu zaben fidda-gwani da jam’iyyar APC na Sanatan Arewacin Yobe ya bar baya da kura, wanda ya jawo a ranar Juma’a daya daga cikin ‘yan takarar, Abubakar Abubakar Jinjiri, ke kalubalantar nasarar da Bashir Sheriff Machina ya samu zuwa kotu.

Hon. Machina wanda ya lashe zaben da kuri’u 289 a zaben, wanda kuma yake sa-toka sa-katsi tsakanin sa da shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan.

  • Ya Yi Yunkurin Arcewa Bayan Daba Wa Mai Ciki Wuka Ta Mutu
  • Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

Haka zalika, bayan da Lawan ya sha kasa a zaben fidda-gwani na shugaban kasa da APC ta gudanar, ya gamu da turjiyar Machina bisa kin janye masa ya ci gaba da jan zarensa a kan kujerar Sanatan Arewacin Yobe, duk da goyon bayan da yake samu daga uwar jam’iyyar APC ta kasa.

A. A Jinjiri yana daga cikin jerin ‘yan takarar da suka mika sunayensu domin kalubalantar zaben fidda-gwani a jihar Yobe, a gaban mai shari’a Fadima Murtala Aminu ta Babbar Kotun Tarayya, da ke Damaturu, babban birnin jihar Yobe.

Da yake zanta wa da manema labarai a gaban kotun, lauyan mai kara, Barists Usman Lukman Nuhu, ya bayyana cewa wanda yake wakilta ya na kalubalantar Machina, tare da uwar jam’iyyar APC ta kasa da ta jihat Yobe, hadi da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), bisa rashin sanya sunan shi a cikin yan takara.

Ya kara da cewa, an hana Jinjiri ya shiga zaben fidda-gwani na Sanatan Arewacin Yobe, duk da kuwa yadda ya halarci wajen da aka gudanar da shi.

“Kuma na yi imani cewa kuna da kofi na takardar sakamakon zaben fidda-gwanin, wanda da kanku na san kun tabbatar babu sunan wanda nake bai wa kariya a takardar sakamakon zaben. ” in ji shi.

Har wa yau, ya ce kin saka sunan dan takara abu ne wanda ya saba wa dokar kundin tsarin mulki ta sashe na (84) da karamin sashe na (3 da 4) na dokokin zabe.

Bugu da kari, akwai kararrakin zaben fidda-gwani guda bakwai wadanda ke kalubalantar sakamakon zaben fidda-gwanin da jam’iyyar APC da ta gudanar.

Haka kuma, mai shari’ar ta ayyana ranar 21 ga watan July 21, 2022 a matsayin lokacin fara shari’ar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
APP Za Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Rashin Takardun Makaranta

APP Za Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Rashin Takardun Makaranta

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version