Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Edo

Zaben fid da gwani na jam’iyyar APC na kokarin fitar da dan takarar gwamna a zaben gwamnan Jihar Edo da zai gudana ranar 21 ga Satumba, ya bar baya da kura, inda a yanzu haka ‘yan takara uku ne ke ikirarin sun yi nasara.

Tun da farko dai, shugaban kwamitin zaben fitar da gwani na APC, Gwamna Hope Uzodinma ya ayyana dan majalisar wakilai, Dennis Idahosa a matsayin wanda ya yi nasara a Otel din Protea da ke Benin, yayin da babban jami’in da ke kula da zaben, Dakta Stanley Ugboaja ya bayyana Sanata Mondaya Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaben a gidan Fasto Osagie Ize-lyamu.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Haka zalika, jami’an da suka kula da zaben fitar da gwanin na kanana hukumomi su ayyana Anamero Sundaya Dekeri a matsayin wanda ya yi nasara.

Mai magana da yawun jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi, Ojo Babatunde, ya sanar da sakamakon zaben ne a daren Asabar, inda ya ce Dekeri wanda ya kasance dan majalisa da ke wakiltar Etsaro a zauren majalisar wakilan Nijeriya, ya samu kuri’u 25,384, wanda ya doke abokin takaransa da ke kusa da shi, Dennis Idahosa da kuri’u 14,127.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na APC, Emmanuel Godwin ya bayyana cewa Gwamna Uzodinma bai da hurumin daukan nauyin da ya rataya a kan jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi.

Da yake mayar da martani kan wannan dambarwar, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC ya dage cewa bisa doka kwamitin da gwamna Uzodinma ke jagoranta shi kadai ne ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fitar da gwani  na APC  Jihar Edo.

Sakataren yada labarai na APC, Felid Morka ya bayyana cewa mutane su yi watsi da duk wani sakamakon da bai cika ka’ida ba.

“Kwamitin gudanarwa na kasa na wannan babbar jam’iyyarmu ya jawo hankalin kan sanar da sakamakon zaben fitar da gwani na APC a Jihar Edo, wanda wasu wadanda ba su da ikon yin haka suke ta yadawa a gidajen talabijin da rediyo da kuma kafafen sada zumunta.

“Muna sanar da cewa kwamitin da Gwamna Hope Uzodinma yake jagoranta ne kadai ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fid da gwani na APC a Jihar Edo bisa tsarin doka.

“Muna kira da ‘ya’yan jam’iyyarmu na jihar da kuma sauran mutane cewa su yi watsi da duk wata sanarwa da ba ta cika ka’idar doka ba,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa dai, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya kafa kwamitin da zai jagoranta zaben fitar da gwani karkashin shugabancin Gwamna Uzodinma a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya ce, “Duk abin da wannan kwamitin ta zantar, to ‘yan takara suna da damar daukaka kara. Domin haka ne ma muke da kwamitin daukaka kara wanda ya kasance kamar kotun koli.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Babban Jami’in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

Babban Jami'in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version