Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC

byYusuf Shuaibu
1 year ago
Ondo

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sanya ranar 20 ga watan Mayu 2024 a matsayin ranar karshe da jam’iyyun siyasa za su mika sunayen wadanda za su tsaya takarar Gwamnan Jihar Ondo.

INEC ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar a lokacin gagarumin taro a shalkwatan hukumar da ke Abuja, wanda ya hada da shugabanni da jiga-jigan mambobin jam’iyyu.

  • Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa
  • Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka

Shugaban hukumar INEC, Farefesa Mahmood Yakubu ya kara jaddada muhimmancin ranar da za a rufe karbar sunayen ‘yan takarar da za su tsaya wa jam’iyyu takarar gwamnan Jihar Ondo.

“Ina kira ga daukacin jam’iyyun siyasa su tabbatar sun aika da ainihin sunayen ‘yan takaransu a daidai lokacin da aka ayyana na ranar karshe 20 ga watan Mayun 2024, a lokacin ne ma shafinmu na yanar gizo za a rufe”.

Taron dai shi ne na biyu a wannan shekarar ta 2024, wanda aka mayar da hankali a kan zabukan da za a yi a jihohi da suka hada da Ondo da Edo da aka tsara a watan Satumba.

Hukumar INEC dai tuni ta kammala buga sunayen ‘yan takarar gwamna da mataimakansu a zaben gwamnan Jihar Edo. Daga cikin wadanda suka halarci wannan muhimmin taro akwai shugaban jam’iyyan APC na kasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje da shugaban jam’iyyar LP, Julius Abure da shugaban jam’iyyar SDP, Shehu Gabam.

Farfesaa Yakubu dai ya yi kira da a tabbata an bi dokokin da hukumar zabe ta tanadar, “Abu ne mai muhimmanci ga dukkanin jam’iyyun siyasa da za su shiga zaben da su tabbatar sun bi dukkanin dokoki da tsare-tsaren da hukumar zabe ta tanadar don tabbatar da cewa an yi zaben cikin lumana”

A daidai lokacin ke karasowa, jam’iyyun siyasa suna ta fadi tashin ganin sun cika ka’idojin da hukumar INEC ta shimfida musu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
EFCC Ta Miƙa Wa FBI $22,000 Da Ta Ƙwato Daga Hannun Masu Satar Kuɗaɗe Ta Yanar Gizo

EFCC Ta Miƙa Wa FBI $22,000 Da Ta Ƙwato Daga Hannun Masu Satar Kuɗaɗe Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version