Zai Yi Wahala A Magance Matsalar Tsaro Matukar… - Janar Lagbaja
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zai Yi Wahala A Magance Matsalar Tsaro Matukar… – Janar Lagbaja

bySulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
lagbaja

Babban Hafsan Sojin Kasa (COAS), Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya ce matukar al’ummar karkara ba su samu ci gaba ba, zai yi wuya a kawo karshen rashin tsaro a Nijeriya.

Dangane da haka, Babban Hafsan ya ce bai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin cin gashin kai, ko shakka babu zai magance matsalar rashin tsaro a kasar nan.

  • Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa
  • Za A Samar Da Asibitin Da Zai Yi Amfani Da Hausa Zalla -Sarkin Hausawan Afrika

Janar Lagbaja ya bayyana haka ne a yayin bikin da sojojin Nijeriya aka gudanar a Jos, Babban Birnin Jihar Filato a ranar Juma’a. Ya kuma jaddada cewa matukar al’ummomin karkara ba su samu ci gaba ba, zai yi wuya a kawo karshen rashin tsaro a kasar.

“Me ya sa jiga-jigan ‘yan siyasa ke bijire wa ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi, wanda jama’a ke kokawa a kai, hanyar da ta fi dacewa wajen kawo ci gaba a matakin kasa shi ne tabbatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi, ba wai ta hanyar kafa kwamitoci ko na ofis ba, mun riga mun kafa ma’aikatu, har sai mun yi aiki, dole a dauki ci gaba zuwa matakin kasa.

“Ga wadanda suka san yanayin Arewa-maso-Gabas, lokacin da aka tura ni Bataliya ta 93 a shekarar 1992, a wancan lokacin abu ne mai sauki a cikin sa’o’i uku ka yi tafiya daga Maiduguri zuwa Munguno, Kukawa da sauran wurare, amma a yau abin ba zai yiwu ba, kyakkyawan shugabanci a matakin kananan hukumomi babu shi a yanzu, kuma wannan shi ne ke kawo rashin tsaro a kasar nan ba wai a yankin Arewa maso Gabas kadai ba, har ma a yankin Arewa ta Tsakiya da sauran yankuna.” Inji Janar Lagbaja.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, a baya gwamnonin jihohi sun ki amincewa da yunkurin bai wa kananan hukumomin kasar cin gashin kai. Sai dai gwamnatin tarayya na yin wani yunkuri na bai wa kananan hukumomin cin gashin kansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
ilimi

Gwamnatin Tarayya Ita Kadai Ba Za Ta Iya Daukar Dawainiyar Kudaden Ilimi Ba – Minista

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version