Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Zaman Lafiyar Nijer Shi Ne Na Nijeriya – Buhari

by Muhammad
February 19, 2021
in LABARAI
1 min read
Zaman Lafiyar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Yusuf Shu’aibu,

A ranar Alhamis ce, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, zaman lafiyar Jamhuriyar Nijar shi ne na Nijeriya kasancewarsu makota na kusa. Domin haka, ya bukaci shugaban kasa mai barin gado Mahamadou Issoufou da mukarraban gwamnatinsa su martaba kundin tsarin mulkin kasar wajen gudanar da zabe karo na biyu a ranar 21 ga watan Fabrairun shekarar 2021.

A cewar kalamun mashawarcinsa ta fannin yada labarai, Femi Adesina, shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake amsar bakuncin tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo wanda shi ne shugaban jagoran kungiyar ECOWAS a kan zaben kasar Jamhuriyar Nijar.

Shugaban kasa Buhari ya taya Sambo murna a matsayin wanda ya jagoranci zaben, inda ba a samu dan takarar da ya yi nasara ba wanda za a gudanar da zagaye na biyu a ranar 21 ga watan Fabrairun shekarar 2021, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

“Makoka na kasa da kasa ko na mutum da mutum yana da matukar mahimmanci, wanda zaman lafiyar makocinka shi ne naka, haka kuma kwanciyar hankalinka shi ne na makocinka,” in ji shugaba Buhari.

Ya yi wa Jamhuriyar Nijar da Sambo da tawagarsa fatan alkairi na gudanar da zabe a karo na biyu a wannan mako.

Shugaban tawagar kungiyar ECOWAS ya bayyana cewa, an gudanar da yakin neman zabe cikin kwanciyar hankali da lumana kamar yadda tsarin jam’iyyun siyasan suka tanada.

A zaben farko dai, tsohon ministan harkokin waje, Mohamed Bazoum shi yake kan gaba da kashi 39.33 daga cikin kuri’un da aka jefa, yayin da tsohon shugaban kasa Mahamane Ousmane yake da kashi 17, wanda dukkansu babu wanda ya sami kashi 50 da zai ba shi damar lashe zaben a jikon farko.

SendShareTweetShare
Previous Post

NEDC Ta Bai Wa Matasa Tallafin Kayan Sana’a A Yobe

Next Post

Majalisar Jigawa Ta Amince Da Hukuncin Kisa Ga Masu Fyaden Da Ke Da Kanjamau … Daurin rai-da-rai ga wadanda ba su da cutar

RelatedPosts

Garkuwa

An Kama Sojan Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Sojoji A Zamfara

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim "An kama wani jami’in soja da budurwarsa...

Aikin Wutar Mambilla  A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

Aikin Wutar Mambilla A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Kungiyar gwamnonin arewa maso gabas sun nuna rashin jin dadin...

Bindiga

Gwamna Ortom Ya Yabawa Umarnin Buhari Na Hana Mallakar  AK47 Ba Bisa Ka’ida Ba

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom a ranar...

Next Post
Hukuncin Kisa

Majalisar Jigawa Ta Amince Da Hukuncin Kisa Ga Masu Fyaden Da Ke Da Kanjamau … Daurin rai-da-rai ga wadanda ba su da cutar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version