• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

by Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihar Zamfara ita ce ta farko a Nijeriya da ta fara amfani da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani (ZDLF) don samar wa al’ummarta muhimman fasahohin zamani don ci gaban tattalin arziki, tsarin gudanar da aiki na zamani, da ƙirƙire-ƙirƙire.

 

A ranar Larabar da ta gabata ne aka gudanar da babban taron masu ruwa da tsaki kan tsarin ilimin fasahar zamani na Zamfara a ɗakin taro na Garba Nadama a Sakatariyar JB Yakubu da ke Gusau, babban birnin jihar.

  • An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
  • Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, taron masu ruwa da tsakin ya haɗa da manyan cibiyoyin gwamnatin tarayya, abokan ci gaba, ’yan majalisa, malamai, da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu domin yin nazari tare da inganta tsarin.

 

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana tsarin a matsayin wani kwakkwaran taswirar zamani da za a sa a gaba tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an aiwatar da shi sosai.

 

Ya ci gaba da cewa, “A yau mun samu wani gagarumin ci gaba a tafiyarmu ta haɗin gwiwa a jihar Zamfara ta hanyar inganta fasahar zamani, ƙirƙire-ƙirƙire, da hanyoyin samun bayanai da fasahar sadarwa.

 

“Tsarin Ilimin Fasahar Zamani nna Zamfara wani tsari ne da zai amfani buƙatun al’umma na dogon lokaci don samar wa mutanenmu ƙarfin aiki da haɓaka ƙwarewarsu a cikin duniyar fasahar zamani.

 

“Kamar yadda muka sani, ilimin fasahar zamani yana da muhimmanci don samar da ayyukan yi da samar da ingantacciyar tsarin aiki. Ba zai yiwu mu rungume hannu mu bar jihar a baya ba a zamani ilimin fasahar zamani.

 

“Wannan tsarin yana da nufin samar da ilimi a bangaren fasahar zamani kan abubuwan da suma shafi – kwamfuta, ayyukan gwamnati, da kasuwanci. Tsarin yana dubi ga jihar da kowane ɗalibi zai ƙware sosai a fannin fasahar zamani, kowane ma’aikacin gwamnati zai samu fasahar zamani don gudanar da aikin sa, kuma manyan ‘yan kasuwa da ƙanana suna da ƙwarewar faɗaɗa kasuwancinsu. Mun fara shirin aiwatar da wannan hangen nesa.

Zamfara

“Jihar Zamfara ta haɗa gwiwa da Kamfanin Oracle domin horar da matasa 3,000 a shirin ‘Cloud 2 Computing, Artificial Intelligence, Data Science, and Database Management’. Tare da makarantar Oracle, manyan makarantunmu za su samu tallafi don yaye ɗalibai masu ƙwarewa a harkar masana’antu.

 

“An fara aiki a Cibiyar Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZIIT) da ke Gusau, wannan cibiya za ta kasance cibiyar ƙwararru ta yanki, da ke ba da ilimin kwamfuta da kuma samar da ƙirƙire-ƙirƙire a cikin gida. Muna da burin ganin mun ɗinke barakar fasahar zamani da kuma sanya Zamfara a matsayin cibiyar ilimin kwamfuta a Arewacin Nijeriya.”

 

Tun da farko, a jawabinsa na maraba sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Nakwada, ya bayyana ƙudirin gwamnatin jihar na ganin jihar Zamfara ta kasance kan gaba wajen kawo sauyi a bangaren fasahar zamani a Arewacin Nijeriya.

 

Da take isar da saƙon fatan alheri, Sanata Ikra Aliyu Bilbis (Sanata mai wakiltar Zamfara ta tsakiya), Shugabar Kwamitin Fasahar Zamani da Tattalin Arziki na Majalisar Dattawa, ta yaba wa Zamfara kan yadda take kan gaba a lokacin da ci gaban ƙasa ya ta’allaka kan fasahar zamani. Sanatar ta ba da gudunmawar kwamfutoci 300 ga ZITDA don tallafa wa tsarin fasahar zamani a duk faɗin jihar.

Zamfara

A jawabinsa dangane da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani na Zamfara (ZDLF), Dokta Habib Gajam, Babban Sakatare na Hukumar Bunƙasa Fasahar Watsa Labarai ta Zamfara (ZITDA), ya bayyana tsarin a matsayin wata dabarar da ta shafi mutane da aka tsara.

 

Muhimman cibiyoyi na fasahar zamani na Gwamnatin Tarayya da aka wakilta a taron masu ruwa da tsakin sun haɗa da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC), Galaxy Backbone, Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA), Cibiyar Kuka da Tauraron Ɗan Adam, da Hukumar Kare Bayanai ta Nijeriya (NDPC).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

Next Post

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

4 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

5 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

7 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

8 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

9 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

10 hours ago
Next Post
Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.