Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Zan Samo Wa Nijeriya Cibiyoyin Koyon Sana’a Daga Jamus —Ambasada Tugga

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauc

Yusuf Mai-Tama Tugga shi ne sabon Jakadar Nijeriya a kasar Jamus wanda shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya tura a kwakin baya, ya shaida cewar kasar Jamus kasa ce da take fama da yawaitar ‘yan Nijeriya masu yin kaura a sakamakon rashin sana’o’in dogaro da kai, ya ce Jamus ta iya fahimtar hauhawar ‘yan Nijeriya masu yin tururuwa zuwa kasar ta su baya rasa nasaba da rashin aikin yi da Nijeriya ke fama da ita. Ya ce kasar ta himmatu waje samar wa Nijeriya cibiyoyin koyon sana’o’in dogaro da kai. A bisa haka ne ya shaida cewar, zai yi kokari wajen kawo wa Nijeriya ci gaba sosai daga kasar ta Jamani. Ya bayyana hakan ne a wajen taron liyafar taya shi murnar samun mukamin da magoya bayansa suka shirya masa a kwanaki kafin tafiyarsa kama aiki a can Jamus

samndaads

Da yake amsa tambayoyin manema labaru a wajen taron, Amasada Yusuf Tugga ya ce, matsalar yawaitar ‘yan Nijeriya masu kaura zuwa Jamus zai ragu da zarar a ka samu hanyoyin koyar da sana’o’in dogaro da kai “Idan mutanen mu suka samu abun yi ne kawai za magance wannan matsalar, shi ya sa na ke cewa su Jamani suna da shiri na kawo cibiyoyin sana’ar dogora da kai, kuma akwai kamfanoninsu da suke da sha’awar kafa hanyoyin koyar da sana’a. kasan ba wai sai wanda ya yi karatu bane kawai zai samu aikin yi don haka wannan zai samar da ragowar masu kaura zuwa Jamani”. In ji sabon Jakadar

Da yake jawabi a kan wakilcin da zai yi wa Nijeriya a kasar Jamus kuwa, Ambasadan ya shaida cewar “Jamus kasa ce mai matukar muhimmanci, tana kuma kan gaba a yankin kasashen Turai. ”Duk da cewa jahohinsu bai kai namu ba, amma babbar kasace, Jamus tana da jahohi 16 ne, sai dai manya ne kuma sun jima suna samun ci gaba ta fuskacin kimiyya, cinikaiyya, kere-kere da kuma ilimi. Sannan sun kasance wacce take da tsohon dangantaka da Nijeriya” in ji shi.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Bukaci Gwamna Lalong Da Ya Yi Garambawul A Shugabancin Jam’iyyar APC

Next Post

Dan Majalisar Tarayya Ya Raba Kwamfutoci A Sakkwato

RelatedPosts

Alaba

‘Yan Kasuwan Arewa A Legas Mu Hada Kai Don Cigaba – Muhammadu Alaba

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Hadin kai shi wani babban al’amari...

Jama'a

Taimaka Wa Jama’a Shi Ne Shugabanci Nagari -Matawalle Alagwadun Legas  

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai,   Matawallen Alagbado, Alhaji Muhammadu ya...

Samarun

Yadda Rasuwar Matashi Ta Jefa Mutane Cikin Alhini A Samarun Zariya

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Idris Umar, A ranar laraba ta wannan makon da...

Next Post

Dan Majalisar Tarayya Ya Raba Kwamfutoci A Sakkwato

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version