Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Zan Taimaka Wa Arsenal Wajen Samun Tikitin Kofin Zakarun Turai – Odegard

by Abba Ibrahim Wada
January 28, 2021
in WASANNI
1 min read
Zan Taimaka Wa Arsenal Wajen Samun Tikitin Kofin Zakarun Turai – Odegard
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dan wasa Martin Odegard wanda ya koma Arsenal daga Real Madrid ya bayyana cewa zai yi iya kokarinsa wajen taimakawa kungiyar wajen samun tikitin gasar cin Kofin Zakarun Turai na Champions League na kakar wasa mai zuwa.

dan wasan mai shekara 22 a duniya dan kasar Norway bai samu lokacin buga wa Real Madrid wasanni sosai ba a karkashin kociyan kungiyar Zinedine Zidane a kakar bana wanda hakan yasa ya nemi tafiya zaman aro domin ci gaba da samun buga wasanni.
kungiyoyin Real Sociedad da Ajad suma sun nuna sha’awar su ta daukar Odegard wanda ya buga wasannin aro a baya a Soceidad din sai dai tuni Arsenal ta cimma yarjejeniya da Real Madrid na daukar dan kwallon da take sa ran kila ya buga mata wasa da Manchester United ranar Asabar.
Wani masannin harkokin wasanni dan kasar Sipaniya, Guillem Balague ya ce Real Madrid ta zabi dan kwallon ya je buga gasar Premier League maimakon Real Sociedad domin zaifi samun irin gogewar da suke bukata.
Kuma zai je Arsenal bayan da Mesut Ozil ya koma Fenerbahce da buga gasar Turkiya wanda aka kai ruwa rana kafin cinikin wanda ya kawo karshen zaman shekara bakwai da rabi da Ozil yayi yana bugawa kungiyar wasa.
Odegard ya koma Real Madrid daga Stromgodset a watan Janairun shekara ta 2015 ya kuma buga wa Real Madrid wasa tara a kakar bana sannan Real Madrid tana ta biyu a teburin Laliga da tazarar maki bakwai tsakaninta da Atletico Madrid mai kwantan wasa daya ita kuwa Arsenal tana ta 11 a teburin Premier League da maki 29, bayan buga karawa 19.

SendShareTweetShare
Previous Post

Laporta Ya Zargi PSG Da Jefa Barcelona Rudani

Next Post

Wane Ne Sabon Kociyan Chelsea, Thomas Tuchel?

RelatedPosts

Guardiola

Yanzu Manchester United Ce Kawai Nake Son Karyawa Wuya – Guardiola

by Abba Ibrahim Wada
11 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Pep Guardiola, ya...

Carlo Ancelotti

Ina Fatan Zuwa Kofin Zakarun Turai A Everton – Carlo Ancelotti

by Abba Ibrahim Wada
11 hours ago
0

Mai horar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Eberton...

Cavani

Na Dawo Da Karfina – Cavani

by Abba Ibrahim Wada
12 hours ago
0

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Manchester United,...

Next Post
Wane Ne Sabon Kociyan Chelsea, Thomas Tuchel?

Wane Ne Sabon Kociyan Chelsea, Thomas Tuchel?

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version