Zanga-zanga: Bauchi Ta Yi Hannun Riga Da Ikirarin Rufe Asibitoci
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Bauchi Ta Yi Hannun Riga Da Ikirarin Rufe Asibitoci

bySulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi ta ce, babu batun wata zanga-zangar tsadar rayuwa a jihar balle zancen rufe asibitoci a fadin jihar. 

 

Sakataren gwamnatin jihar Bauchi, Barista Muhammad Ibrahim Kashim ne ya sanar da matsayar gwamnati a yayin da yake ganawa da ‘yan jarida a ranar Laraba.

  • Sakataren Gwamnati Da Ministoci Na Ganawar Sirri Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa 
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci ‘yan Nijeriya Da Su Soke Zanga-Zangar Da Suka Shirya

Idan za a tuna, wani jami’in gwamnatin jihar a jiya (Talata) ya shelanta cewa, su na da wani bayanin da ke cewa, akwai shirin kai hari ga asibitoci a ranar gudanar da zanga-zanga kan matsin rayuwa da ake ciki, don haka gwamnatin ta dauki matakin cewa za ta kulle dukkanin kananan asibitoci (PHCs) da suke fadin jihar a ranar zanga-zangar.

 

Sai dai a martaninsa, sakataren gwamnatin, ya ce wannan jami’in ya yi gaban kansa wajen sanar da batun rufe asibitoci kuma za a hukuntasa daidai da abun da ya yi.

 

Kan hakan, Ibrahim Kashim ya gargadi duk wani ko wasu da ke shirin gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa da cewa, ya tafi wata jiha dai ba Baachi ba, don haka ba batun zanga-zanga a jihar.

 

Ya ce: “Na tabbatar ku na da rahotonnin da ke zagawa cikin jihar nan da ma kasa cewa, gwamnatin jihar Bauchi ta ba da dama a rufe asibitocinta a cikin jihar da kananan hukumomi saboda zanga-zangar da ake shirin yi.

 

“Na daya dai, jihar Bauchi ba mu yarda da zanga-zangar nan ba kuma ba za a yi ba. Wanda ya ke da niyyar yin zanga-zanga sai dai ya je ya yi a wani waje ba dai Bauchi ba, mu Bauchi an sanmu da zaman lafiya. Kuma mu a gwamnatance mun dauki kudurin cewa za a cigaba da zaman lafiya.

 

“Game da maganar rufe asibitoci, shi din ma ba za a yi ba. Wanda ya ba da wannan labarin ya fada ne kawai albarkacin bakin sa kuma za a hukuntashi kamar yadda doka ta tanada.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Me Ya Sa Aka Yi Taron Sulhu Tsakanin Mabambantan Bangarori Na Palasdinu a Beijing?

Me Ya Sa Aka Yi Taron Sulhu Tsakanin Mabambantan Bangarori Na Palasdinu a Beijing?

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version