Zanga-Zanga: NSCDC Ta Shirya Aikewa Da Jami'ai 30,000 Faɗin Nijeriya
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-Zanga: NSCDC Ta Shirya Aikewa Da Jami’ai 30,000 Faɗin Nijeriya

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Zanga-Zanga

Shugaban hukumar tsaro ta NSCDC, Dr. Audi, ya umarci a rarraba jami’ai 30,000 a duk faɗin ƙasa kafin zanga-zangar da aka shirya gudanarwa daga ranar 1 zuwa 10 ga Agusta. A cikin taron gaggawa da aka gudanar a Shalƙwatar NSCDC a Abuja, Dr. Audi ya jaddada buƙatar jami’an su kasance masu ƙwarewa da ladabi da kuma bin ƙa’idojin.

Ya jaddada cewa yayin da ‘yan ƙasa ke da haƙƙin yin zanga-zanga cikin lumana, ba su da haƙƙin lalata kadarorin gwamnati. Jami’an da za a tura za su kasance ƙarƙashin kulawar shugabannin yanki da kwamandojin Jihohi a jihohi 36 da FCT.

  • Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja
  • Ba Zamu Lamunci Zanga-Zangar Tashin Hankali Ba – IGP 

Dr. Audi ya gargaɗi jami’an da su guji duk wani aiki na zalunci ko take haƙƙin ɗan adam, yana jaddada cewa NSCDC ba za ta lamunci duk wani abu da zai ɓata sunanta ba. Ya bayyana muhimmancin kare muhimman kadarorin ƙasa da gine-ginen gwamnati daga yiwuwar lalata su yayin zanga-zangar.

Bugu da ƙari, Dr. Audi ya yi kira ga matasan Nijeriya da su guji ayi amfani da su wajen aikata duk wani mummunan aiki, yana ba da shawarar tattaunawa maimakon ayyukan assha da za su jawo da na sani. Ya jaddada aniyar hukumar na haɗa kai da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da zaman lafiya da ƙarfafa tsarin tsaron ƙasa.

A cikin jawabin sa, Dr. Audi ya yi kira da a yi zanga-zangar cikin lumana idan dole sai an yi, yana tunatar da zanga-zangar baya da ta haifar da tashin hankali, da lalata dukiya, da kuma rasa rayuka.

Ya umarci jami’ai da su tabbatar zanga-zangar ta kasance cikin lumana kuma su kare gine-ginen gwamnati daga ‘yan daba. Shugaban NSCDC ya tabbatar da cewa hukumar tana da ƙwazo wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, tare da inganta zaman lafiya da kuma bunƙasa tsaron ƙasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Arsenal Ta Kammala Ɗaukar Riccardo Calafiori Daga Bologna

Arsenal Ta Kammala Ɗaukar Riccardo Calafiori Daga Bologna

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version