Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Hadi Sirika

Alleged N2.8bn Fraud: EFCC Opens Case Against Sirika, Others

Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika Gaban Kotu

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa, EFCC, ta fara tuhumar tsohon ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da wasu mutane uku, bisa zargin almundahanar Naira biliyan 2.6.

Sirika, tare da ɗiyar sa Fatima, Jalal Sule Hamma, da kuma Al-Duraq Investment Limited, suna fuskantar tuhume-tuhume guda shida da suka haɗa da zamba a ofis da kuma badaƙalar kwangila a babbar kotun birnin tarayya (FCT) dake Maitama.

  • Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Shaidu na farko na EFCC, Azubuike Okorie, tsohon ma’aikacin ma’aikatar sufurin jiragen sama, ya shaida rawar da ya taka a matsayinsa na Daraktan saye da sayarwa da kuma mataimaki na musamman ga Ministan, inda ya bayyana ayyukan sa na sa ido da tantance ayyuka, duk da cewa ba shi da hannu kai tsaye wajen bayar da kwangila.

Okorie ya bayyana cewa kwamitin aiwatar da ayyukan da ya jagoranta ya gano rashin jituwa a lokacin da ake sa ido kan ayyukan musamman a filin jirgin saman Katsina, inda babu wani ɗan kwangila da yake gudanar da aiki ciki har da Al-Duraq, duk da cewa akwai sunayensu matsayin ƴan kwangila.

Ya shaida cewar har ya kammala aikin gwamnati a watan Mayun 2023, ba a aiwatar da aikin kwangilar da kamfanin Al-Duraq ba wacce ta kai Naira miliyan 800. Ya ƙara da cewa, yana da masaniyar wani kuɗi da aka biya wa Al-Duraq kashi 30 cikin 100 na tara kuɗaɗen shiga, amma babu hannun shi cikin tsarin biyan kuɗi wanda aka yi shi bisa ƙa’ida ba.

Kanu Agabi, SAN, Lauyan Sirika, ya buƙaci da a ɗage zaman domin duba takardun ƙarar, buƙatar da wasu lauyoyin masu ƙara suka goyi bayan kuma masu gabatar da ƙara ba su yi hamayya ba.

Sakamakon haka, Mai shari’a Sylvanus Oriji ya ɗage sauraron ƙarar har zuwa ranar 30 ga wata domin yi masa tambayoyi da kuma ci gaba da shari’ar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version