Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Zidane Ya Ce Real Madrid Na Bukatar Dan Wasan Gaba

by Muhammad
January 11, 2021
in WASANNI
2 min read
Madrid
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, Zinadine Zidane, ya bayyana cewa dole kungiyarsa tana bukatar dan wasa mai zura kwallo a raga biyo bayan canjaras din da tawagar tasa ta buga a daren Asabar da kungiyar Osasuna a gasar La liga.

Real Madrid tana ci gaba da saka kaimi domin ganin ta samu nasarar lashe gasar La liga ta kasar Ingila kuma da ace ta samu nasara a wasan na ranar Asabar zata zama ta daya akan teburin gasar sai dai duk da haka  kungiyar za ta buga gasa uku cikin watan Janairun shekara ta 2021 da suka hada da La Liga da Spanish Super Cup da kuma Copa del Rey.

samndaads

Real Madrid wadda take ta biyu a teburin La liga ta shiga shekarar 2021 da kafar dama, bayan da ta doke kungiyar kwallon kafa ta Celta Bigo daci 2-0 a gasar Spaniya ranar biyu ga watan Janairu a filin wasa na Alfredo Di Stefano sai dai ta kasa doe Osasuna a wannan satin da ya gabata.

A watan na Janairu kungiyar za ta fafata a karawa uku a La Liga, da daya a gasar Spanish Super Cup wanda ta lashe a bara a Saudiyya da kuma fafatawa a gasar cin kofin Copa del Rey wato gasar cin kofin kalubale na kasar.

“Tabbas akwai karancin zura kwallo a raga a wannan tawagar tamu saboda haka muma fatan nan gaba kadan zamu samu dan wasan gaba wanda zai taimaka mana saboda zura kwallo a raga yayi kadan a wannan kungiyar” in ji Zidane

Sai dai an tambayi mai koyarwar ko zasu shiga kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa a wannan watan na Janairu domin sayan dan wasan gaba amma Zidane din bai fayyace abinda yake nufi ba hakan yasa ake ganin watakila kungiyar ta iya sayan dan wasan gaba guda daya ko kuma ta karbi aro zuwa karshen kaka.

A kwanakin baya kociyan kungiyar, Zinadine Zidane, ya bayyana cewa ‘yan wasan kungiyar za suyi iya kokarinsu wajen ganin sun farantawa magoya bayan kungiyar rai ta hanyar lashe kofi duk da cewa har kawo yanzu ‘yan wasa basa shiga kallon wasan.

Zidane ya kalubalanci ‘yan wasan da su dage wajen zura kwallo a raga domin hakkin kowanne dan wasa ne yayi kokarin zura kwallo a raga domin taimakawa kungiyara wajen cikar burinta na lashe kofi a bana.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dole Pochettino Ya Nemi Hadin Kan Neymar Da Mbappe – Nazari

Next Post

Hukumar Kididdiga Ta Kasa Ta Yarda An Samu Karin Farashin Kayan Abinci

RelatedPosts

Lukaku

Za Mu Iya Lashe Gasar Siriya A – Lukaku

by Sulaiman Ibrahim
22 hours ago
0

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Inter Milan,...

Pogba

Mun Shirya Doke Liverpool, Cewar Pogba

by Sulaiman Ibrahim
23 hours ago
0

Dan wasan tsakiyar kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Paul...

Mourinho

Mourinho Ya Caccaki ‘Yan Wasansa

by Sulaiman Ibrahim
23 hours ago
0

Kociyan kungiyar Tottenham, Jose Mourinho ya koka da rashin kokarin...

Next Post
Kayan Abinci

Hukumar Kididdiga Ta Kasa Ta Yarda An Samu Karin Farashin Kayan Abinci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version