Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Zidane Ya Sake Caccakar ‘Yan Jarida

by Muhammad
February 21, 2021
in WASANNI
2 min read
Zidane
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta  Real Madrid, Zinedine Zidane ya sake caccakar ‘yan jaridun kasar Sipaniya a karo na biyu sannan ya bukaci da su rika fadin gaskiya idan zasu rubuta labari akan Real Madrid sannan ya ce har yanzu Real Madrid tana fafatawa a gasar La Liga kuma zasu ci gaba da cin wasanni domin samun nasarar lashe gasar ta bana.

Real Madrid tana mataki na uku akan teburin gasar La liga, inda take bayan kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid, wadda ke saman teburin da maki shida kuma duk da haka Real Madrid ta fi ta yawan buga wasa sannan yadda kungiyar ta gaza yin katabus a ‘yan kwanakin nan ya sa kafafen watsa labari sun soma caccakar Zidane, dan kasar Faransa da nuna gazawa.

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid dai tana fama da koma baya a wannan kakar wanda hakan yasa aka fitar da ita daga gasar cin kofin Copa Del Rey duk da cewa wasu suna ganin rashin ‘yan wasa masu lafiya ne yake kawowa kungiyar tarnaki.

“Abin da yake ba ni dariya shi ne yadda kuke tambaya ta me ya sa nake fushi bai kamata ‘yan jarida ku rika yi min abin da kuke yi min ba mun dauki kofi a kakar wasan da ta wuce domin haka ina ganin ya kamata ku mutunta ni” in ji Zidane a taron manema labarai a kwanakin baya.

Ya kara da cewa “Ba wai mun shekara 10 ba ne (da daukar kofi), a kakar wasan da ta wuce ne kuma akalla ya kamata ku mutunta mu kan abubuwan da muka samu nasara a kansu ku (‘yan jarida) kun cika surutu sannan me ya sa ba za ku kalle ni ido da ido ku gaya min cewa kuna so a kore ni daga kungiyar nan ba, ba a bayan idona ba.”

An sake nada Zidane a matsayin kociyan Real Madrid a watan Maris na shekarar 2019, bayan ya jagoranci kungiyar wajen daukar kofin Zakarun Turai sau uku a jere da kuma kofin lig a kakar wasa ta shekarar 2016 zuwa 2017 lokacin shugabancinsa na farko.

Dan kasar Faransa mai shekara 48 a duniya zai jagoranci kungiyar a fafatawa da kungiyar da ke kasan teburin gasar La Liga Huesca bayan Real Madrid ta sha kashi a hannu Lebante koda yake bai halarci wasan ba saboda ya kamu da cutar korona

“An killace ni tsawon mako biyu, na matsu na fito na kuma nuna wa duniya cewa zan jajirce har zuwa karshe kuma yanzu na dawo domin ci gaba da jagorantar wannan kungiya zuwa ga nasara kamar yadda na saba a baya,” in ji shi.

Sergio Ramos bai fafata ba a wasan da kungiyar ta buga saboda raunin da ya ji, a yayin da Zidane ya sanya masu tsaron raga uku a tawagarsa mai mutum 17 kuma ‘yan wasa Eden Hazard da  Dani Carbajal da Federico Balberde da Rodrygo da Lucas Vazquez su ma ba su shiga karawar ba saboda jinya, ya yin da aka dakatar da Eder Militao.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ba Da Gudunmuwar Alluran Riga Kafi 100,000 Ga Kasar Namibia

Next Post

Ina Fatan Arsenal Zata Kammala Kakar Wasan Bana Da Kofi -Ozil

RelatedPosts

Atletico

Za A Yi Kare Jini Biri Jini Tsakanin Real Madrid Da Atletico Gobe

by Muhammad
17 hours ago
0

A ranar Lahadi ne Real Madrid za ta ziyarci filin...

Bale

Real Madrid Ce Kawai Zata Fayyace Makomar Gareth Bale -Mourinho

by Muhammad
17 hours ago
0

Kocin kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Jose Mouinho ya ce,...

Sevilla

Daman Nasan Muna Da Nasara A Kan Sevilla -Messi

by Muhammad
17 hours ago
0

Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona, Leonel Messi, ya...

Next Post
Ozil

Ina Fatan Arsenal Zata Kammala Kakar Wasan Bana Da Kofi -Ozil

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version