Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Zuba Hannun Jari: Gwamnatin Jihar Katsina Da Gaske Ta Ke Yi. –Maryam Katagun

by
2 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
Shirin Dawo Da Martabar Katsina: Ina Mu Ka Dosa?
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

ADVERTISEMENT

Wata muhimmiyar ganawar sirri da ta gudana tsakanin jami’an gwamnatin jihar Katsina da kuma tawagar ministan ma’aikatar harkokin masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta Najeriya na nuni da cewa zata haifar da da mai ido dangane da kafa kamfanin zaka a garin Funtua.
Wannan ganawa na da nufin samar da wani kyakkyawan yanayi ta fuskar kasuwanci da kuma zuba hannun jari ga ‘yan kasuwa na waje da na cikin gida, ta hanyar samar da katafaran kamfanin zaka da za a kafa masana’antu a jihar Katsina.
Da take jawabi ga manema labarai a Katsina ministan harkokin masana’antu da kasuwanci da zuba jari Maryam Katagum ta bayyana irin dangantakarr da take tsakanin ma’aiktarta da kuma gwamnatin jihar Katsina, inda ta ce daga cikin abubuwa da za su duba a jihar akwai abubuwan da gwamnatin Katsina ta samar musamman a garin Funtua domin asassa mana’antu
Ta kara da cewa za su kai ziyara a wajan da gwamnati ta samar domin ganewa idanunsu abubuwan da ke kasa da suka hada da layin wutar lantarki da hanyoyin sufuri.
“Acikin wannan tattaunawa da muka yi, mun yi bayani akan tsarin aikin da zamu yi, ba wai duba wuri kawai ba, zamu sanya masu tuntuba domin yin abinda ya kamata da kuma kyakyyawan nazari akan wannan aiki, kuma muna bukatar masu ruwa da tsaki a cikin wannan shiri, wanda hakan zai baiwa masu zuba hannun jari damar zuwa jihar Katsina” inji ta
Haka kuma ta kara da cewa acikin wannan tattaunawa da suka yi sun amince cewa za su ziyarci wannan katafaran wuri da gwamnatin jihar ta samar domin kafa masana’anta a garin Futua domin gani da ido ya fi labari.
Sai dai a nashi jawabin mataimakin gwamnan jihar Katsina, Alhaji Mannir Yakubu ya bada tabbacin goyan bayan gwamnatin Aminu Bello Masari akan baban shiri, inda ya ce sun shirya tsaf domin bada gudunmawar da ake bukata.
Haka kuma ya kara da cewa sun ji dadi matuka dangane da wannan tattaunawa da suka yi da ministan masana’antu, kasuwanci da zuba jari, inda ya ce wannan ne karo na farko da suka taba ganawa da wata mininta har tsawo awa biyu akan mahimman abubuwa da suka shafi jihar Katsina.
“Mune muka fara kai ziyara har ofishinki, amma tun daga wancan lokacin babu abinda ya faru sai bayan wata shida, amma yanzu gashi mun fara wannan aikin da zai iya canza yanayin tafiyar tattalin arzikin jihar Katsina, muna da fatan cewa katafaran kamfanin saka na Funtua wanda gwamnatin tarayya ta amince da shi sai zama mai amfani a garemu” inji shi
Alhaji Mannir Yakubu ya kara da cewa gwamna Aminu Bello Masari ya amince da bada kadada 140 domin a gudanar da wannan aikin na gina kamfanin saka na Funtua, ya ce sai daga bayan suka lura cewa wannan aikin yana bukatar baban wuri wanda yanzu haka sun kara mika kokon baranmu domin karin wani filin, inda ya ce suna da fatan cewa za a samu karin so sai.
Haka kuma ya godewa ministan da ‘yan tawagarta bisa nuna damuwar da jihar Katsina da kuma wannan muhimmin aiki da suka sa gaba na samar da katafaran kamfanin Zaka a garin Funtua wanda ya ce cikin karamin lokacin anyi abubuwa da dama.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Tabbatar Da Wanzuwar Sabbin Masarautu  A Kano Tare Da Yin Watsi Da karar Masu Nadin Sarakuna

Next Post

Aikin Lauya Aiki Ne Na Jin kai Ga Al’umma– Barr. Adamu Fagge

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
3 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
3 days ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
3 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
5 days ago
0

...

Next Post
Aikin Lauya Aiki Ne Na Jin kai Ga Al’umma– Barr. Adamu Fagge

Aikin Lauya Aiki Ne Na Jin kai Ga Al'umma-- Barr. Adamu Fagge

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: