Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Zai Bunkata Harajin Gwamnati – Hadiza Usman

by Yusuf Shuaibu
December 31, 2020
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Hadiza Usman
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Zuba jari a tashoshin ruwa zai yi matukar bunkasa bangaren bakin takun kasar nan tare da karin haraji ga gwamnatin tarayya. Shugabar hukumar kula da tashoshin ruwan Nijeriya (NPA), Hadiza Bala-Usman ita ta bayyana haka lokacin da take kira a kan akwai bukatar kara farfado da bangaren tashoshin ruwa da ke fadin kasar nan. Shugabar hukumar NPA ta bayyana cewa, kayayyakin more rayuwa da gwamnati ta gina a tashoshin da kadarorin da aka samu a karkashin shugabancinta sun yi matukar bunkasa tashoshin bakin ruwan Nijeriya wanda ya kara kudaden shiga a bangaren tashoshin jiragen ruwa.

“Dokin cimma burikanmu, muna bukatar kara samun manyan jiragen ruwa wadanda za a yi amfani da su a tashoshin,” in ji ta.

samndaads

Ta kara da cewa, domin samun damar aiwatar da ayyuka yadda suka kamata a dukkan tashoshin jiragen ruwa, hukumomi sun yi kokarin ci gaba da fadada kayayyakin aiki, domin kara inganta gudanar da ayyuka.

“An gudanar da wannan kokari ne domin tabbatar da dukkan tashoshin bakin teku guda shiga su kasance suna aiki yadda ya kamata a kowani lokaci.

A nasa bayanin, ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya bayyana cewa, babu wanda yake musun cewa, tashoshin jiragen ruwa suna da matukar mahimmanci ga banfaren tattalin arziki, a lokacin da aka saka dokar hana zirga-zirga a cikin wata uku da suka gabata, a wannan lokacin ne aka gane mahimmancin bangaren tashoshin ruwa a cikin kasar nan.

“A yanzu haka, gwamnati tana kokarin bunkasa sauran fannonin tattalin arziki domin rage dogaro da bangaren mai da gas, mun san rawar da bangaren tashoshin jiragen ruwa suke takawa a cikin kasar nan musamman ma a bangaren farfado da tattalin arziki a cikin wannan gwamnati.

SendShareTweetShare
Previous Post

Nijeriya Na Tsammanin Samun Tiriliyan N2.8 A Sabon Aikin Gas

Next Post

Rashin Adalci Ne Muraran A Ce Ina Kira A Yi Juyin Mulki – Bishop Kukah

RelatedPosts

Kangin Talauci

Shirin Tsamo Mutane Miliyan Biyu Daga Kangin Talauci Ya Kankama – Osinbajo

by Yusuf Shuaibu
3 days ago
0

Bayan samun nasarar kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki...

Talakawan Nijeriya

Talakawan Nijeriya Miliyan 24.3 Sun Samu Tallafin Naira 5,000 Kowanne – Ministar Jinkai

by Yusuf Shuaibu
3 days ago
0

A ranar Talata ne, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, sama...

FIRS

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

by Yusuf Shuaibu
4 days ago
0

Hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS) ta bayyana cewa, ta...

Next Post
Bishop Kukah

Rashin Adalci Ne Muraran A Ce Ina Kira A Yi Juyin Mulki – Bishop Kukah

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version