Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

Zulum Ya Bai Wa Hukumar NYSC Gudunmawar Miliyan N400 A Borno

by Muhammad
March 24, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
NYSC
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

Darakta Janar a hukumar kula da masu yi wa kasa hidima ta Nijeriya reshen jihar Borno (NYSC)- Birg. Janar Shu’aibu Ibrahim, ya ce cikin shekaru biyu, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya bayar da umurnin were sama da naira miliyan 400 don tallafa wa hukumar wajen kula da jin dadin daliban masu aikin bautar kasa a fadin jihar.

Babban jami’in hukumar ya bayyana haka ranar Litinin a birnin Maiduguri a bukin yaye dalibai kimanin 269 da suka samu kwarewa a fannin yanayin kasa (Soil Doctors and Edtension), yayin da kuma ya yaba wa Gwamnan bisa wannan namijin kokari wanda ya ce ya cancanci yabo da godiya.

A hannu guda kuma, shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Lawan, wanda ya wakilci shugaban kasa Muhammadu Buhari a taron yaye daliban, ya jinjina wa Gwamna Zulum dangane da wannan kokarin.

Ya ce, Gwamnan ya yi abinda ya dace a yaba masa dangane da wannan babbar hobbasa ce wajen kyautata alakar gwamnatin sa da hukumomin gwamnatin tarayya da ke aiki a jihar, wanda hakan ya dace matuka.

Sanata Lawan ya kara da cewa duk da kalubalen da Gwamna Zulum ya sha fuskanta a kokarinsa na dawo da al’amurra kan turba a jihar tsakanin shi da yan ta’adda, hakan bai sanya gwiwarsa ta yi sanyi ba balle ya razana a wannan manufa tashi ta kokarin inganta rayuwar al’ummar jihar Borno.

A jawabinsa, Babban Sakataren hukumar kula da ci gaban yanayin kasa ta NALDA, Mista Paul Ikonne, a taron ya bayyana Gwamna Zulum daya daga cikin jajirtattun gwamnoni nagari wadanda ba su da abokin burmi a fadin kasar nan.

Ya ce babban abin a yaba ne irin wannan kokari na Gwamna wajen samar da ingantaccen filayen noma a karkashin shirin samar da ayyukan noma ga matasa a jihar.

Bugu da kari, wadannan matasa wadanda su ka samu horo na musamman, kumanin 269 wadanda kuma su ka fito daga kananan hukumomi 27 da ke fadin jihar Borno. An horar da su hanyoyin binciken yanayin kasa a karkashin shirin samar da matasan manoma ta hanyar hadin gwiwa tsakanin hukumar NALDA da ma’aikatar kula da dabbobi da bunkasa kiwon Kifi a jihar.

A bayaninsa, Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya bayyana cewa akwai bukatar kwararru a wannan fanni na yanayin kasa domin sake farfado da ayyukan noma a Nijeriya.

A hannu guda kuma, Zulum ya yaba da kokarin gwamnatin da ta gabace shi a karkashin jagorancin Sanata Kashim Shettima, wanda ya ce, gwamnatinsa ce ta dora harsashi mai inganci a fannin ayyukan noma a jihar

SendShareTweetShare
Previous Post

Kananan Masana’antu Milyan 40 Ake Da Su A Nijeriya – SON

Next Post

Sojojin Nijeriya Sun Yi Gargadi Ga Igboho Da Masu Ikirarin Raba Kasa

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by Sulaiman Ibrahim
2 weeks ago
0

Daga Abdullahi Muh’d, Kano Shugaban Gidauniyar ‘Charity’ mai rajin tallafa...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Zubairu M Lawal, A yayin da uwar jam'iyyar APC...

Next Post
Igboho

Sojojin Nijeriya Sun Yi Gargadi Ga Igboho Da Masu Ikirarin Raba Kasa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version