Sulaiman Ibrahim">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Zulum Ya Nemi Kiristoci Da Su Yi Addu’a Ga Sojoji, ‘Yan Banga Da Sauransu

by Sulaiman Ibrahim
December 25, 2020
in LABARAI
1 min read
Zulum Ya Nemi Kiristoci Da Su Yi Addu’a Ga Sojoji, ‘Yan Banga Da Sauransu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamna Babagana Zulum na Borno, a ranar Juma’a a Maiduguri, ya umurci ‘yan Nijeriya da su yi addu’a ga sojoji, masu sa kai na kungiyar Hadin gwiwar kungiyoyin farar hula, wadanda suka bace da wadanda suka yi gudun hijira sakamakon tashin hankalu, a yayin da suke bikin Kirsimeti.
“Yayin da nake yiwa kowa fatan bikin Kirsimeti cikin lumana, farin ciki da albarka, ina rokon dukkan mu da muyi tunani kan yadda jami’an tsaro, mafarautan cikin gida da ‘yan banga ke yin bikin Kirsimeti a cikin daji, suna farautar Boko Haram sannan kuma maharan suma suna farautar su.
“Ya dace mu ma muyi tunani kan yadda iyalan wadannan dakaru da masu sa kai ke yin bikin ba tare da iyalansu da ‘yan uwansu ba, ” in ji gwamnan a sakon Kirsimeti.
“Yin tunani a kan yanayin ‘yan uwansu zai tayar da hankalinmu don sake sadaukar da kai ga yin addu’o’i ba tare da tsayawa ba don samun zaman lafiya da kuma tallafawa jami’an tsaro dake yaki da masu tayar da kayar baya ta hanyar samar da bayanai masu dacewa ga jami’an tsaro,’ ‘in ji shi.
“Za mu ci gaba da ba da goyon baya ga jami’an tsaro, musamman wadanda suka nuna kwazo.
“Za mu yaba kuma mu ba da lada, kuma a inda ake bukatar tayar da jijiyoyin wuya za muyi hakan, duk a madadin ‘yan kasa da muka rantse za mu kare hakkinsu. ” in ji Gwamna Zulum.

SendShareTweetShare
Previous Post

Rundunar Soji Ta Kara Yawan Dakarunta Akan Babbar Hanyar Damaturu Zuwa Maiduguri

Next Post

Korar Tuchel Za Ta Iya Hana Mbappe Komawa Real Madrid

RelatedPosts

Da Dimi-diminsa: Buhari Ya Sauya Shugabannin Rundunonin Tsaro

Da Dimi-diminsa: Buhari Ya Sauya Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
14 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da murabus din shugabannin...

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Sulaiman Ibrahim
22 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Sulaiman Ibrahim
22 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Next Post
Tuchel

Korar Tuchel Za Ta Iya Hana Mbappe Komawa Real Madrid

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version