Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Zulum Ya Tallafa Wa Manoma Da ’Yan Gudun Hijira 11,200 A Damasak

by Muhammad
January 12, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Damasak
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

A kokarinsa wajen saukaka wa jama’ar da matsalar tsaro ta shafa a yankunan karkara, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya kai ziyarar a garin Damasak, shalkwatar karamar hukumar Mobbar a arewacin jihar, inda a ranar farko ya kaddamar da tallafin kayan noman rani ga manoma 1,200 don bunkasa ayyukan gona da wadata jihar da abinci.

samndaads

A rana ta biyu a garin na Damasak, Zulum ya gudanar da raba kayan abinci ga yan gudun hijira kimanin 10,000, wanda kowane mutum daya ya samu tallafin buhun shinkafa mai nauyin 25kg, buhun wake 25kg, buhun masara 25kg tare da lita biyar na man girki don saukaka musu kuncin rayuwa.

Gwamna Zulum ya ziyarci yanki tare da rakiyar Sanata mai wakiltar arewacin jihar Borno a zauren majalisar dattawa kana kuma dan asalin garin Damasak, Hon. Abubakar Kyari, wanda ya raba injinan bayin ruwa, takin zamani, iraruwa, magungunan kashe kwari hadi da kyautar naira 5000 ga kowane manomi domin bunkasa noman rani da yankin ya shahara dashi.

Ya ce wannan daya daga cikin manufofin Gwamna Zulum, wanda a kowane lokaci burinsa shi ne sake tsugunnar da jama’a tare da tallafa musu don samun hanyoyin dogaro da kai wanda hakan zai taimaka wajen magance matsalolin da jama’a ke fuskanta tare da dogaro da kai.

A nashi bangaren, Gwamna Zulum ya bukaci manoma a garin Damasak, da sauran yankunan jihar da cewa su yi kokari wajen habaka aikin noma wajen noma abinci da dogaro da kai wanda hakan zai taimaka wajen rage dogaro daga kungiyoyin jinkai.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Likitoci 15 Sun Kamu Da Korona A Nasarawa

Next Post

’Yan Bindiga Sun Halaka ‘Yan Sanda Uku A Caji Ofis Din Ebonyi

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Bindiga

’Yan Bindiga Sun Halaka 'Yan Sanda Uku A Caji Ofis Din Ebonyi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version