Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Zuwa Aiki A Makare: Za Mu Fara Ladabtar Da Malamai A Kebbi –Magawata Aliero

by Tayo Adelaja
October 5, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin-kebbi

Kwamishinan ilimi na Jihar Kebbi, Alhaji Muhammad Magawata Aliero, ya umurci shugabanin makarantun Sakandare na cikin Jihar da su kai rahoton duk wani malamin makaranta da ya ƙi zuwa wurin aiki akan lokaci.

Alhaji Magawata Aliero ya bada wannan umurni ne lokacin da ya yi, wani taron gana wa da shugabannin makarantun Sakandare da ke a cikin Jihar Kebbi a ɗakin taro na masauki Shugaban ƙasa da ke Birnin-kebbi a jiya. Inda ya ja hankalin malaman makarantun na jihar da su guji ƙin zuwa wajen aiki ko zuwa a makare da kuma tashi kafin lokaci.

Kwamishinan ya ce, gwamnatin Jihar Kebbi tana bayar da fifiko ga ɓangaren ilimi musamman ilimin firamare da Sakandare. Ya kuma umurci daraktoci da sakatarorin ilimi na jihar da su ɗauki matakin ladabtarwa ga duk malamin da aka samu ba ya gudanar da aikinsa ta yadda ya kamata.

Ita ma Sakatariyar Ma’aikatar ilimi ta jihar, Hajiya Rafa’atu Noman Garba Hammani, ta kari da Jan hakalin shugabanin makarantun Sakandare da cewa baza mu yi ƙasa a gwiwa ba ga bin tsarin da kwamitin ilimin na ƙasa ya fito dashi ba, saboda haka ta ce, duk wanda ya bari aka kama shi da karya dokar da aka shata, toh ya sani cewa za a ladabtar da shi ko ita. Ta ci gaba da cewa ta yi umurni ga shugabannin makarantun da duk wanda ke zama a gidan makaranta kuma ba cikin makarantar ya ke aikinsa na koyar wa ba, toh a tayar da shi ko wanene, kuma a bai wa malamai na makaranta wannan gidan domin malami indan baya da gida toh ba ka tunanin za ya iya tsayawa domin gudanar da aikinsa ta yadda ya kamata.

Daga nan kwamishinan ya godewa shugabanin makarantun ga amsa kiran da yayi mu domin ganawa da kuma irin goyun bayan da suke bayar wa ga ci gaban ilimi a jihar ta Kebbi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kakakin Majalisar Dokokin Kano Na Iya Fuskantar Kiranye

Next Post

‘Yan Gudun Hijira 79 Suka Amfana Da Shirin Kamfanin PAN

RelatedPosts

Tuhumar Malam Abduljabbar Za A Yi, Ba Mukabala Da Shi Ba– Sheikh Khalil

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja Shugaban Majalisar Malamai na Shiyyar...

ISWAP

Boko Haram Ta Yi Garkuwa Da Ma’aikatan Jinkai Bakwai A Dikwa

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri A harin bayan nan da mayakan...

Makanike

Shari’ar Gonaki: Kotu Ta Aike Wa Rundunar Soja Da Ma’aikarar Shari’a Sammaci

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Isa Abdullahi Gidan ‘Bakko, Zariya Kotun daukaka kara dake...

Next Post

‘Yan Gudun Hijira 79 Suka Amfana Da Shirin Kamfanin PAN

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version