Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya

byAbubakar Sulaiman
2 weeks ago
Tsaro

A ƙalla jami’an tsaro 53 aka kashe a faɗin Najeriya cikin makonni biyu da suka gabata, bisa ga ƙididdigar da Daily Trust ta tattara daga rahotannin kafafen watsa labarai. Waɗanda aka kashe sun haɗa da Sojoji, da ƴansanda, da jami’an NSCDC, da na shige-da-fice da na haraji, da kuma na sa-kai, da mambobin JTF da ƙungiyoyin tsaron al’umma na jihohi. Wannan adadi bai haɗa da rahotannin da ba a bayar ba.

Yawancin jami’an an kashe su ne yayin da suke amsa kiran kai hari kan al’umma, yayin da wasu kuma aka yi musu kwanton ɓauna a wuraren binciken ababen hawa da sansanonin tsaro. Manyan hare-haren kwanan nan sun faru ne a jihohin Biniwe da Kogi, inda ƴan bindiga suka hallaka jami’an ƴansanda bakwai da wasu jami’an tsaro a hare-hare dabam-dabam tsakanin Juma’a da Lahadi. Haka kuma an yi garkuwa da wasu jami’an a lamarin da ya auku a Binuwe

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa 9 NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Waɗannan kashe-kashen sun ƙara haskaka yadda barazanar tsaro ke ta ƙara jawo asarar rayukan jami’an tsaro a Nijeriya. Binciken da Daily Trust ta gudanar a watan Disambar 2024 ya nuna cewa an kashe a ƙalla ƴan sanda 229 daga Janairu 2023 zuwa Oktoba 2024 sakamakon hare-haren ƴan bindiga, da na masu tada kayar baya, masu al’ada da kuma ƴan fashi da makami. Sabbin hare-haren sun nuna cewa tashin hankali na ƙaruwa duk da yunƙurin samar da tsaro da ake ci gaba da gudanarwa.

A martanin Hukumar DSS, ta gurfanar da mutane tara a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja a makon jiya kan zargin hannu a kisan da aka yi kwanan nan a jihohin Binuwe da Filato. Cikin waɗanda aka gurfanar har da Haruna Adamu da Muhammad Abdullahi daga Jihar Nasarawa, bisa zargin hannu a kisan gilla da aka yi a Guma LGA ta Benue.

Haka kuma an gurfanar da Terkende Ashuwa da Amos Alede bisa zargin ramuwar gayya da ta haddasa lalata kadarori da rasa shanu 12 a ƙauyen Ukpam. DSS ta kuma gurfanar da wani mutum daban kan mallakar bindigogi M16 guda bakwai ba bisa ƙa’ida ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version