Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba

byAbdullahi Faruk
2 years ago
Kebbi

Sabon Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kebbi, Alhaji Faruk Musa Yaro Enabo, ya bai wa Gwamna Nasir Idris da al’ummar Jihar tabbacin gudanar da aikin Hajji nagari.

Shugaban ya nuna matukar godiya ga Gwamna Idris bisa samun sa da ya cancanci a nada shi a irin wannan matsayi mai girma, inda ya yi alkawarin sauke dimbin amanar da aka dora masa.

  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi
  • Ku Yi Aiki Tukuru Ko Na Kore Ku, Tinubu Ga Ministoci

Shugaban hukumar ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar ragamar jagorancin hukumar a Birnin Kebbi, da kuma yin jawabi ga ma’aikatan hukumar da masu fatan alheri.

Shugaban ya gode wa Allah da ya ba shi wannan aiki na addini mai daraja, sannan ya sanya fata da amana, shi domin shiriya da taimako don sauke nauyin da ke kansa da matukar nasara.

Alhaji Faruk Musa ya bayyana sauran mambobin hukumar a matsayin fitattun mutane, inda ya ba da tabbacin cewa za su fara aiki nan take domin samun kyakkyawan aikin Hajji na aikin hajji mai zuwa.

Haka kuma ya yi bayanin tsarin bizar da kasar Saudiyya ta yi na aikin Hajjin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa, sabanin abin da aka samu a baya na wahalar da ake fuskanta na ba da biza cikin kankanin lokaci, bayar da bizar ga maniyyata daga yanzu zai dogara ne kan biyan kudin aikin Hajji gaba daya.

Sai dai ya bayyana cewa da zarar duk wani mahajjaci ya biya kudinsa gaba daya, hukumomin kasar Saudiyya za su ba shi bizar, inda ya ce tuni aka bude hanyar shiga ta kuma za a rufe bayan mako uku.

Shugaban ya sanar da duk mai niyyar zuwa aikin Hajji cewa makonni biyu kacal a cikinsu su biya kudin aikin Hajjin da ya kai Naira miliyan 4.5 sannan ya bukace su da su gaggauta biya.

Tun da farko, a jawabin maraba Alhaji Sani Idris Abarshi, sakataren hukumar ya bayyana farin cikinsa da nadin Faruq Musa Yaro Enabo a matsayin shugabanta, inda ya bayyana shi a matsayin wanda ya kware da kwazo.

Alhaji Sani Abarshi, ya yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da Alhaji Faruk Musa wajen tafiyar da harkokin Hukumar Jin Dadin Alhazai, inda ya yi alkawarin ba shi dukkan goyon baya da hadin kai don samun nasara.

Cikin wadanda suka raka shugaban domin karbar ragamar mulki har da shugaban jam’iyyar APC na jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Muhammad Kana Zuru da dimbin masoya da abokan arziki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version