• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba

byAbdullahi Faruk
2 years ago
Kebbi

Sabon Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kebbi, Alhaji Faruk Musa Yaro Enabo, ya bai wa Gwamna Nasir Idris da al’ummar Jihar tabbacin gudanar da aikin Hajji nagari.

Shugaban ya nuna matukar godiya ga Gwamna Idris bisa samun sa da ya cancanci a nada shi a irin wannan matsayi mai girma, inda ya yi alkawarin sauke dimbin amanar da aka dora masa.

  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi
  • Ku Yi Aiki Tukuru Ko Na Kore Ku, Tinubu Ga Ministoci

Shugaban hukumar ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar ragamar jagorancin hukumar a Birnin Kebbi, da kuma yin jawabi ga ma’aikatan hukumar da masu fatan alheri.

Shugaban ya gode wa Allah da ya ba shi wannan aiki na addini mai daraja, sannan ya sanya fata da amana, shi domin shiriya da taimako don sauke nauyin da ke kansa da matukar nasara.

Alhaji Faruk Musa ya bayyana sauran mambobin hukumar a matsayin fitattun mutane, inda ya ba da tabbacin cewa za su fara aiki nan take domin samun kyakkyawan aikin Hajji na aikin hajji mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Haka kuma ya yi bayanin tsarin bizar da kasar Saudiyya ta yi na aikin Hajjin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa, sabanin abin da aka samu a baya na wahalar da ake fuskanta na ba da biza cikin kankanin lokaci, bayar da bizar ga maniyyata daga yanzu zai dogara ne kan biyan kudin aikin Hajji gaba daya.

Sai dai ya bayyana cewa da zarar duk wani mahajjaci ya biya kudinsa gaba daya, hukumomin kasar Saudiyya za su ba shi bizar, inda ya ce tuni aka bude hanyar shiga ta kuma za a rufe bayan mako uku.

Shugaban ya sanar da duk mai niyyar zuwa aikin Hajji cewa makonni biyu kacal a cikinsu su biya kudin aikin Hajjin da ya kai Naira miliyan 4.5 sannan ya bukace su da su gaggauta biya.

Tun da farko, a jawabin maraba Alhaji Sani Idris Abarshi, sakataren hukumar ya bayyana farin cikinsa da nadin Faruq Musa Yaro Enabo a matsayin shugabanta, inda ya bayyana shi a matsayin wanda ya kware da kwazo.

Alhaji Sani Abarshi, ya yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da Alhaji Faruk Musa wajen tafiyar da harkokin Hukumar Jin Dadin Alhazai, inda ya yi alkawarin ba shi dukkan goyon baya da hadin kai don samun nasara.

Cikin wadanda suka raka shugaban domin karbar ragamar mulki har da shugaban jam’iyyar APC na jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Muhammad Kana Zuru da dimbin masoya da abokan arziki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version