Yadda Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Asibitin Ƙauran Namoda Da Ya Inganta
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Asibitin Ƙauran Namoda Da Ya Inganta

byLeadership Hausa
1 year ago
gwamna

A ranar Talatar nan ne Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda, wanda aka yi masa gyara, tare da wadata shi da kayan aikin kula da lafiya.

Babban asibitin, yana kula da Ƙauran Namoda da maƙwabtanta, wanda kuma aka wadata shi da kayan aiki don ya samar da iingantacen kiwon lafiya.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa babban asibitin, an samar masa da kayan aikin kula da lafiya, waɗanda suka haɗa da na’urorin binciken cututtuka, gadajen haihuwa, na’urar auna bugun zuciya (ECG), na’urorin binciken jini, babbar na’urar binciken jini ta ‘automatic hematology analyzer’, na’urar auna nauyi ta zamani, fitilar haskawa yayin aikin tiyata da dai wasu kayan kula da lafiya da daman gaske.

Sanarwar ta ƙara da cewa, asibitocin gaba ɗaya na da matuƙar muhimmanci wajen samar da ingantaccen kiwon lafiya, wanda ya kamata ya zama mai sauƙi ga al’ummar Jihar Zamfara.

A wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya nanata cewa babban abin da gwamnatinsa ta mayar da hankali a kai shi ne farfaɗo da taɓarɓarewar ababen more rayuwa da magance matsalolin da ke addabar dukkanin sassan tattalin arzikin jihar.

gwamna

“Wannan hangen nesa ya sa muka yanke shawarar samar da ajandar kawo sauyi da ta ƙunshi ginshiƙai shida, inda kiwon lafiya ya kasance ginshiƙi na uku, biyo bayan ilimi da tsaro.

“Manufarmu na farfaɗo da asibitoci shi ne mu tabbatar da cewa an samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga jama’ar mu, walau a yankunan karkara ko a birane. Wannan fahimtar ta sa muka gyara tare inganta cibiyoyin kiwon lafiya da suka lalace, musamman a garuruwa masu muhimmanci irin su Kaura Namoda, da ke a tsakanin ƙananan hukumomi da kuma zama wuri mafi sauƙi ga yankunan da ke kewaye.

“Na yi farin cikin bayar da rahoton cewa, a cikin watanni 14 da suka gabata, mun samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari wajen gyara da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar nan.

gwamna

“Har ila yau, mun kammala shirye-shiryen ɗaukar ma’aikatan kiwon lafiya da horar da su, sayen magunguna da kayan aiki masu muhimmanci, da gabatar da ayyukan kula da lafiyar mata da yara kyauta.

“Muna fatan waɗannan ayyukan za su haifar da ingantacciyar lafiya ga jama’armu ta hanyar rage mace-macen mata masu juna biyu, mace-macen jarirai, da daƙile cututtuka a faɗin jihar.

  • Badakalar Kudade: Kotun Daukaka Kara Ta Nemi Tsohon Gwamnan Kogi Ya Gurfanar Da Kansa A Kotu

 

“Bikin ƙaddamarwar na yau ya nuna aniyarmu ta samar da ingantaccen kiwon lafiya ga ɗaukacin mazauna Zamfara, ba tare da la’akari da wurinsu, matsayinsu ko kuɗin da suke samu ba.

“Tsarin aikin ya haɗa da sake gyara asibitin gaba ɗaya, tare da samar da tsayayyen wutar lantarki mai ƙarfin 32 kW, da sanya fitulun titi 25, da kuma samar da muhimman kayan aiki ga likitoci. Bayan kammala wannan ginin cikin nasara, ina da yaƙinin cewa mutanen Kaura Namoda da garuruwa da ƙauyukan da ke maƙwabtaka da su, yanzu za su samu damar cin moriyar kiwon lafiya mai sauƙi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?
Kiwon Lafiya

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
Matsalar Tasgadewar Kashin Baya
Kiwon Lafiya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Next Post
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

An Kama Dan Uwan Kwankwaso Da Wasu 4 Kan Badakalar Magani A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version