Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa 'Yan Takara Gwajin Miyagun Kwayoyi A Kano
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa ‘Yan Takara Gwajin Miyagun Kwayoyi A Kano

bySadiq
1 year ago
Kano

Hukumar Zabe ta Jihar Kano (KANSIEC), ta ce za ta gudanar da gwajin shan miyagun kwayoyi a kan dukkanin ‘yan takarar shugabancin kananan hukumomi da kansiloli da za su shiga zabe.

Shugaban hukumar, Farfesa Sani Lawal Malumfashi ne, ya bayyana wannan lokacin da ya ziyarci hedikwatar Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), a Kano ranar Talata.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Budewar Dandalin Mata Na SCO
  • Gwamnatin Borno Ta Kafa Sansanin Kula Da Wadanda Ambaliya Ta Shafa

Farfesa Malumfashi, ya bayyana cewa KANSIEC za ta duba dukkanin ‘yan takarar da ke neman shugabancin kananan hukumomi da kansiloli don tabbatar da cewa ba su yi amfani da kwayoyi ba.

Ya roki NDLEA ta taimaka wajen gudanar da gwajin kuma ta aike da sakamakon ga KANSIEC, wanda za su yi amfani da shi wajen tantance cancantar ‘yan takarar.

Ya tabbatar da cewa hukumar zaben a jihar tana da niyyar hana wadanda ke amfani da kwayoyi samun iko a kananan hukumomi.

Ya kuma yi gargadi cewa zaben wadanda ke amfani da kwayoyi a shugabancin kananan hukumomi zai kara tabarbarewar matsalar ta’ammali da kwayoyi da kuma iya jefa kananan hukumomi cikin talauci ta hanyar ta’azzara amfani da miyagun kwayoyi da aikata laifuka masu alaka da kwayoyi.

Farfesa Malumfashi, ya kuma nemi goyon bayan NDLEA wajen tabbatar da tsaro yayin zabe da bayan zabe.

A martaninsa, Kwamandan NDLEA na Jihar Kano, Abubakar Idris Ahmad, ya tabbatar wa shugaban hukumar cewa rundunarsa a shirye ta ke ta bayar da dukkanin goyon baya da hadin kai don gudanar da zabe ba tare da matsala ba a jihar.

A cikin bayanin da Bashir Habib Yahaya, Daraktan Wayar da Kan Jama’a na KANSIEC, ya yi, ya bayyana cewa taron ya hada da gabatar da ka’idojin zabe da jadawalin zabe ga NDLEA, domin sanin ta inda za ta bayar da gudunmawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Wani Asibiti A Kano Ya Ƙaddamar Da Na’urar Kula Da Jarirai Irinta Ta Farko A Arewacin Nijeriya

Wani Asibiti A Kano Ya Ƙaddamar Da Na'urar Kula Da Jarirai Irinta Ta Farko A Arewacin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version