• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa ‘Yan Takara Gwajin Miyagun Kwayoyi A Kano

bySadiq
1 year ago
Kano

Hukumar Zabe ta Jihar Kano (KANSIEC), ta ce za ta gudanar da gwajin shan miyagun kwayoyi a kan dukkanin ‘yan takarar shugabancin kananan hukumomi da kansiloli da za su shiga zabe.

Shugaban hukumar, Farfesa Sani Lawal Malumfashi ne, ya bayyana wannan lokacin da ya ziyarci hedikwatar Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), a Kano ranar Talata.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Budewar Dandalin Mata Na SCO
  • Gwamnatin Borno Ta Kafa Sansanin Kula Da Wadanda Ambaliya Ta Shafa

Farfesa Malumfashi, ya bayyana cewa KANSIEC za ta duba dukkanin ‘yan takarar da ke neman shugabancin kananan hukumomi da kansiloli don tabbatar da cewa ba su yi amfani da kwayoyi ba.

Ya roki NDLEA ta taimaka wajen gudanar da gwajin kuma ta aike da sakamakon ga KANSIEC, wanda za su yi amfani da shi wajen tantance cancantar ‘yan takarar.

Ya tabbatar da cewa hukumar zaben a jihar tana da niyyar hana wadanda ke amfani da kwayoyi samun iko a kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Ya kuma yi gargadi cewa zaben wadanda ke amfani da kwayoyi a shugabancin kananan hukumomi zai kara tabarbarewar matsalar ta’ammali da kwayoyi da kuma iya jefa kananan hukumomi cikin talauci ta hanyar ta’azzara amfani da miyagun kwayoyi da aikata laifuka masu alaka da kwayoyi.

Farfesa Malumfashi, ya kuma nemi goyon bayan NDLEA wajen tabbatar da tsaro yayin zabe da bayan zabe.

A martaninsa, Kwamandan NDLEA na Jihar Kano, Abubakar Idris Ahmad, ya tabbatar wa shugaban hukumar cewa rundunarsa a shirye ta ke ta bayar da dukkanin goyon baya da hadin kai don gudanar da zabe ba tare da matsala ba a jihar.

A cikin bayanin da Bashir Habib Yahaya, Daraktan Wayar da Kan Jama’a na KANSIEC, ya yi, ya bayyana cewa taron ya hada da gabatar da ka’idojin zabe da jadawalin zabe ga NDLEA, domin sanin ta inda za ta bayar da gudunmawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Wani Asibiti A Kano Ya Ƙaddamar Da Na’urar Kula Da Jarirai Irinta Ta Farko A Arewacin Nijeriya

Wani Asibiti A Kano Ya Ƙaddamar Da Na'urar Kula Da Jarirai Irinta Ta Farko A Arewacin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version