Kungiyar Lauyoyin Musulmi ta Kasa (MULAN) reshen Jihar Kaduna, ta yi Allah wadai da kisan gillar da aka yi wa matafiya a Jihar Filato, inda ta bayyana harin a matsayin rashin tausayi da imani.
Kungiyar ta yi Allah wadai ne a wata sanarwa da shugaban kungiyar, Barista Awwal Tesleem Shittu ya raba wa manema labarai a Kaduna.
- Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
- Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
A cewar sanarwar, harin ya faru ne a ranar Juma’a, 20 ga watan Yuni, 2025, lokacin da wata motar bas mai kujeru 18 dauke da fasinjoji daga Basawa na Jihar Kaduna.
“Muna tunawa, da bakin ciki, irin wannan ta’asa da aka yi a baya, inda aka yi wa matafiya da ba su ji ba gani ba, kwanton bauna ba tare da an hukunta su ba.”
Sanarwar ta kara da cewa sake faruwar hare-haren da aka tsara da kuma niyya, musamman a Jihar Filato, alama ce mai hatsarin gaske da ke nuna cewa masu aikata laifuka da ‘yan ta’adda suna sake kwarin gwiwa sakamakon gazawar gwamnati na ci gaba da aiwatar da rashin bin doka da oda
“Muna bayar da wannan a matsayin gargadi kai tsaye ga gwamnatin Nijeriya a matakin tarayya da na jihohi. Ka da a bari a zubar da jinin wadannan ‘yan Nijeriya marasa laifi ya tafi a banza.”
Shittu, ya lura da cewa hakurin al’ummomin da ake ci gaba da yi wa kisan gilla ba shi da iyaka, ya kara da cewa rashin kamawa da gurfanar da masu aikata laifukan tare da hukuntansu yana nuna gazawar gwamnati.
“Muna bukatar a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa, kuma na gaskiya kan wannan kisan kiyashi da kamawa tare da gurfanar da duk wadanda ke da alhakin wannan danyen aikin.
“Muna san a biya isasshiyar diyya ga iyalan wadanda abin ya shafa, haka kuma a tura jami’an tsaro na dindindin a duk wuraren da ake kisa a Filato da jihohin makwabta.
“Akwai bukatar gwamnatin tarayya ta kara zage damtse na ganin ta magance yawaitar kashe-kashen da ake yi a fadin kasar nan baki daya” in ji sanarwar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp