Wani sakamakon binciken ra'ayin jama'a da cibiyar bincike ta Pew ta fitar...
Read moreDetailsLokacin da injuna suka fara tunani, yaya dan adam zai yi mu’amala...
Read moreDetailsA kwanan baya, kamfanin Nearpays na kasar Najeriya ya lashe kyaututtuka a Afirka da ma duniya baki daya, saboda manhajar biyan kudi ta wayar salula da ya tsara, wadda ta kunshi fasahar kirkirarriyar basira ko AI. Wani abu na musamman da ke cikin wannan manhajar shi ne yadda ya iya aiki ba tare da amfani da yanar gizo ko Intanet ba, wanda ke ba mutane damar biyan kudi ta wayar salula, ko da a yankunan karkara masu nisa inda ba a samun siginar wayar salula. Wannan hanyar amfani da fasaha wajen inganta rayuwar jama’a ta yi daidai da ka'idar amfani da fasahar AI ta Majalisar Dinkin Duniya ta "Fasaha mai fifita al’umma, amfani da AI ta hanyar da ta dace", kuma ra'ayi ne da kasar Sin ke kokarin aiwatarwa a fannin raya fasahar AI. A kasar Sin, babban burin da ake neman cimmawa ta hanyar amfani da fasahar AI shi ma ya kasance samar da hidimomi ga jama’a. Idan aka dauki misali da bangaren kula da lafiya, a wasu asibitoci na matakin unguwanni a birnin Beijing, na’urorin aiki masu kunshe da fasahar AI na iya taimaka wa marasa lafiya tsara shirin ganin likita, da tantance cututtukan ido, da kuma taimaka wa likitoci wajen neman bayanan tarihin jinya, da tantance hotunan da aka dauka ta na’urorin bincike, da kuma kula da magunguna. Ta wannan hanya, an daidaita aikin jinya a asibitocin, da kuma samar da sauki ga marasa lafiya. A zahiri, "Dora mihimmanci kan moriyar jama’a" wani tunani ne na bai daya na Sin da Afirka ta fuskar fasahar AI. Sai dai mabambantan kasashe su kan samu ra’ayoyi masu bambanci. Misali, yanayin da ake ciki a Amurka ya bambanta. Cikin wata makalar da ya rubuta, masanin ilimin al’amuran duniya dan kasar Kenya Elijah Mwangi ya bayyana bambanci da ke tsakanin salon kasar Sin da na Amurka a fannin raya fasahar AI. Ya bayyana cewa dabarar raya fasahar AI ta Sin ta shafi manufar sanya gwamnati ta rika ba da jagoranci, da kokarin samar da na’urorin zamani a matsayin ababen more rayuwa, yayin da Amurka ke bin tsarin jari-hujja. Wato masana'antun fasahar AI na Amurka galibinsu manyan kamfanoni ne ke kula da su bisa tsarin kasuwanci. A ganin wadannan kamfanoni, damar samun riba da takara da kamfanonin sauran kasashe, sun fi bauta wa jama’a muhimmanci. Idan aka dauki fannin kiwon lafiya a matsayin misali, Amurka tana kokarin amfani da fasahar AI wajen inganta wani tsarin kiwon lafiya mai tsada, maimakon bai wa talakawa damar samun hidimomi masu araha. Wannan babban bambanci ne ya sa kasar Sin fara gabatar da manufar kula da ayyukan raya fasahar AI mai amfanar da al’ummun duniya, wadda ta kunshi ra’ayoyin "Raya fasahar AI don samar da alfanu, da tsaro, da adalci", da "Ba da taimako ga kasashe masu tasowa" , da "Tabbatar da wakilcin kasashe masu tasowa a fannin kula da fasahar AI", da sauransu. Daga gabatar da "Shawarar kula da harkoki masu alaka da fasahar AI na duniya" , zuwa aiwatar da "Shirin raya fasahar AI mai amfanar da kowa", kasar Sin tana kokarin mai da fasahar AI wani lamari da zai amfanar da dukkan bil'adama. A lokacin da ake magana kan fasahar AI ta kasar Sin, masana ilimin kimiyya da fasaha ’ya’yan Afirka su kan yaba mata bisa yadda take da araha. Elijah Mwangi ya ce, karfin kasar Sin a fannin kera kayayyaki, ya sanya ta zama bangare mai muhimmanci dake samar da hidimomi masu araha ga masu amfani da fasahar AI. Wannan ya saukaka wa kasashen da ke son amfani da fasahohin zamani kuma a farashi mai rahusa. A nasa bangare, Lawrence Nderu, wani shehun malami dake aiki a jami'ar kimiyya da fasaha masu alaka da aikin gona ta Jomo Kenyatta ta kasar Kenya, ya yaba wa manhajojin fasahar AI na kasar Sin, wadanda suka zama “Open Source”, wato nuna dukkan bayanan tsara manhaja ba tare da boye su ba. Ya ce bisa amfani da wadannan manhajojin kasar Sin, kungiyoyi masu tsara manhaja na kasashen Afirka za su iya kara dogaro da kai, da kare bayanai masu mahimmanci, da kuma samar da dabarun daidaita matsalolin da ake fuskanta a kasashen Afirka. Yadda ake amincewa da tunani da fasahohi masu nasaba da AI na kasar Sin shi ma ya inganta hadin gwiwar Sin da Afirka. A Afirka ta Kudu, kamfanonin kasar Sin sun ba da taimako wajen daidaita tsarin kula da zirga-zirgar jiragen kasa, wanda ya tabbatar da tsaro. A Djibouti, tsarin ba da gargadi don kandagarkin bala’i na "MAZU-Urban", wanda hukumar kula da ayyuka masa alaka da yanayi ta kasar Sin ta bayar kyauta, ya taimaka wajen rage mummunan tasirin bala’i daga Indallahi ga tattalin arziki da rayuwar mutane. Wadannan lamuran sun nuna cewa "dora muhimmanci kan moriyar jama’a" ra’ayi ne na bai daya na Sin da Afirka dagane da aikin raya fasahar AI. Bugu da kari, wannan ra’ayin ya tabbatar da kyakkyawar makoma ga yunkurin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka. (Bello Wang)
Read moreDetailsA farkon watan Yuli, sakamakon guguwar "Maysak" da ta afku, an sami...
Read moreDetailsCi gaban bangaren kimiyya da fasaha ya kasance tamkar "kashin baya" ga wata kasa. Dole ne a samu kashin baya mai karfi, kafin daga bisani kasar ta iya kawar da shingen da ya hana ta samun ci gaba mai dorewa a bangaren tattalin arziki. A kwanan nan, an gudanar da babban taron shekara-shekara na karrama masu nazarin kimiyya da fasaha a kasar Sin, inda mutane biyu suka samu lambobin yabo na matsayin koli, kana masana kimiyya da fasaha masu gudanar da wasu ayyuka 258 su ma sun samu lambobin yabo. Wadannan ayyuka sun shafi ilimin wasu bangarori na tushe, wadanda ke samar da taimako wajen biyan bukatar kasar Sin ta raya wasu manyan tsare-tsare, ko kuma haifar da alfanu ga al'ummar kasar. A wajen taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping da kansa ya mika lambobin yabon ga mutanen da aka karrama, kana ya yi wani jawabi, inda ya bukaci a karfafa hadin gwiwa tsakanin sassa da hukumomi na Sin a fannin kirkiro sabbin fasahohi, da inganta cudanya tsakanin bangarorin nazarin kimiyya da fasaha da masana'antu, da kara kokarin horar da matasa, da kyautata tsarin kula da kimiyya da fasaha da tabbatar da tsaro, da dai sauransu. Jawabin shugaba Xi ya nuna yadda shugabannin kasar Sin suke fahimtar batun nazarin kimiyya da fasaha, da jagoranci mai nagarta da suke samarwa a wannan fanni. To, sai dai, wane tasiri ci gaban bangaren kimiyya da fasaha na kasar Sin ke da shi ga duniya, musamman ma kasashen Afirka? Dangane da wannan tambaya, wani jami'i mai kula da harkokin waje na kasar Najeriya mai suna Raymond Delmut ya ba da amsa, ta hanyar rubuta wata makala, wadda aka wallafa a shafin yanar gizo na jaridar "the Sun" ta Najeriya. Cikin bayaninsa, Mista Delmut ya ce, yanzu haka kasar Sin na sauya salonta daga "mai samar da hajoji" zuwa "mai kirkiro sabbin fasahohi". Saboda haka salon hadin gwiwar Sin da Afirka shi ma zai sauya, daga mai dogaro kan aikin gini da ciniki, zuwa nau'in da zai fi dora muhimmanci kan kirkire-kirkire, da ci gaban masana'antu, da musayar ilimi. A cewarsa, ci gaban bangaren kimiyya da fasaha na kasar Sin dama ce ga kasashe masu tasowa ta raya tattalin arziki, maimakon barazanar takara. Hakika, ta hanyar tantance sakamakon da aka samu a kasashen Afirka, bisa hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin kimiyya da fasaha, cikin sauki za mu iya fahimtar nagartaccen tasirin da kasar Sin ta yi. Misali, a Najeriya, wasu kwararru masu ilimin aikin gona na kasar Sin sun kirkiro wani sabon nau'in shinkafa, wanda ya sa yawan shinkafar da a kan girba cikin gonar da fadinta ya kai eka 1, ya karu daga ton 5.6 zuwa ton 8. Kana a kasar Morocco, tashar samar da wutar lantarki ta makamashin hasken rana da wani kamfanin kasar Sin ya gina tana samar da wutar lantarki mai tsabta ga miliyoyin magidanta. Ban da haka, cibiyar tattara alkaluman labarin kasa ta Sin da Afirka tana samar da hidimar gargadin kare kai daga bala'u ga kasashe 54 dake nahiyar Afirka, yayin da sabon tsarin biyan kudi na zamani da aka gina a tsakanin bangarorin Sin da Afirka ya sa abun da ake kashewa wajen biyan kudi yayin gudanar da ciniki raguwa da fiye da kaso 30%. Haka zalika, allunan sola kirar kasar Sin suna samar da damar amfani da wutar lantarki ga karin mutane a sassa daban daban na nahiyar Afirka. Ta wadannan misalai za mu san cewa, "kashin bayan" kimiyya da fasaha na kasar Sin ya riga ya zame wa kasashen Afirka abin dogara. (Bello Wang)
Read moreDetailsA farkon rabin shekarar bana, sakamakon yakin da ya barke tsakanin Amurka...
Read moreDetailsRanar 6 ga watan Yuli ita ce ranar raya kauyuka ta duniya....
Read moreDetailsA yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD(UNHRC) karo na 62, asusun bunkasa hakkin dan Adam na kasar Sin ya shirya wani taron gefe. A gun taron, wani masanin Sin ya yi maganar da ta burge kowa, inda ya ce, "Ma'auni na gaske dake tantance yanayin hakkin dan Adam na wata kasa, ba wani tsari ba ne, sai dai ko al’ummar wannan kasa suna rayuwa da mutunci da tabbaci da kuma ci gaba." Bisa nazarin da aka yi, na ce, tun daga shekara ta 2009, Sin ta tsara da aiwatar da shirye-shiryen raya ayyukan hakkin dan Adam na kasa, wanda hakan ba wai kawai ya nuna alkawarin da ta yi wa al'ummarta da duniya ba, har ma ya samar da abin koyi ga kasa da kasa kan jagorantar harkokin hakkin dan Adam. Alkaluma sun nuna cewa, a shekara ta 2025, jimillar GDP na Sin ya kai sama da Yuan tiriliyan 140, kuma matsakaicin kudin shiga na kowane mutum a ko wace shekara ya kai Yuan 43,377, wanda ya karu da kashi 5.0%, idan aka kwatanta da shekarar da ta gabace ta. Adadin wadanda suka shiga inshorar ritaya mai tushe ya kai mutane biliyan 1.076, adadin da ya kiyaye matsayin kashi 95%. Karin guraben aikin yi da aka samar a wannan shekara ya kai miliyan 12.67. Yawan masu shiga karatun tilas na tsawon shekaru 9 na kasar ya kuma kiyaye kashi 96.1%, kuma adadin daliban da ke karatu a jami’o’i ko kwalejoji ya wuce miliyan 43. Wadannan alkaluma sun shaida nasarorin da kasar ta samu a kokarinta na tabbatar da hakkin al’ummarta, kuma suna nuna yadda take aiwatar da manufar "sanya muradun jama’a a gaban komai" da kuma kare "’yancin rayuwar Sinawa". A yankin Xizang na kasar Sin, a da yawan mutanen da ke fama da jahilci ya kai sama da kashi 95%, amma yanzu an gina cikakken tsarin samar da ilimi na zamani, kuma ana aiwatar da manufar ba da ilimin kyauta na shekaru 15, wanda ya shafi daga matakin gidan renon yara zuwa sakandare. Tsawon rayuwar mutane a yankin ya kuma karu daga shekaru 35.5 a shekarar 1951 zuwa shekaru 72.19 a yanzu. A yankin Xinjiang na Sin, gwamnatin yankin ta kokarin bunkasa masana'antar noma, kamar noman auduga da kuma noman 'ya'yan itatuwa na musamman, don inganta amfani da filayen karkara da kuma kara kudin shigar manoma. A wasu yankuna, an gina makarantun koyon sana'o'i, inda ake ba da horo na musamman kamar aikin lantarki, aikin gida, da kasuwanci ta yanar gizo, don bai wa manoma da makiyaya damar koyon ilmin masana'antu. Wadannan alkaluma da al’amura na bayyana yadda kasar Sin ke kokarin tabbatar da hakkin dan Adam. Tun bayan kafuwar kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD shekaru 20 da suka gabata, har yanzu akwai sauran rina a kaba wajen kula da hakkin dan Adam na duniya. Ayyukan kare hakkin dan Adam na Sin sun ba da mafita madaidaiciya, wato hakkin dan Adam ba hujjar sukar sauran kasashe ba ne, a'a, dabara ce ta samun ci gaba, wato misali girbin gona da kudin shigar jama'a da karatun yara a makarantu, kana da ayyukan yi masu dorewa da ingantuwar rayuwar al’umma. Misalin da Sin take bayarwa dangane da rayuwa da muradun jama’a, ya zama mai ma’ana wajen murnar cika shekaru 20 da kafuwar kwamitin. Wannan kuma ita ce mafi kyawun matakin dake bayyana "Hakkin dan Adam na dukkan bil'adama". (Marubuciya: MINA)
Read moreDetailsLokacin da ake magana kan jam'iyyar da ke mulki a kasar Sin,...
Read moreDetailsA ranar 1 ga watan Yulin 2026, Jam’iyyar Kwaminista Kasar Sin (JKS)...
Read moreDetails© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.