• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

by Muhammad
2 years ago
Sojoji

Hedikwatar tsaron Nijeriya, ta bayyana cewa dakarunta da hadin guiwar sauran hukumomin tsaro sun ceto ‘yan makaranta 137 da aka sace a Kuriga da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

Daraktan yada labarai na rundunar, Manjo Janar Edward Buba, ya ce yaran da aka ceto sun hada da mata 76 da maza 61 da safiyar Lahadi 24 ga Maris, 2024, a wani wuri a jihar Zamfara.

  • An Sako Ɗaliban Makarantar Kuriga Da Aka Sace A Kaduna – Uba Sani
  • Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna

Idan ba a manta ba LEADERSHIP HAUSA a ranar 7 ga Maris, 2024 ta rawaito muku yadda wasu ‘yan ta’adda suka kai hari makarantar LEA Kuriga, karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, inda suka yi awon gaba da ‘yan makaranta 287.

Gwamnatin tarayya dai ta umurci sojoji da su tabbatar an dawo da yaran makaranta lafiya.

A baya LEADERSHIP ta kawo rahoto kan cewa an kubutar da daliban, a cewar gwamnan jihar Uba Sani, wanda ya sanar da farko game da ceto yaran ba tare da bayyana adadin wadanda abin ya shafa ba a safiyar yau Lahadi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Sai dai a cewar sanarwar ta hedikwatar tsaron Nijeriya ta cfurta ya saba da alkaluman farko na adadin daliban da sojojin suka ce sun yi nasarar kubutar da su.

“A ranar Lahadi, 24 ga Maris, 2024, sojojin da ke aiki tare daw hadin guiwar wasu hukumomi sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

“Wadanda aka yi garkuwa da su daga makarantar da ke Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

“Dalibai 137 da aka yi garkuwa da su sun hada da mata 76 da maza 61, an ceto su ne a jihar Zamfara kuma za a mika su ga gwamnatin jihar Kaduna,” inji Manjo Janar Buba.

Rundunar sojin ta ce za a ci gaba da kokarin har sai an gano ragowar mutanen da aka yi garkuwa da su da tabbatar da an kama ’yan ta’addar an yi musu an gurfanar da su gaban shari’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.