• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar tsaron Nijeriya, ta bayyana cewa dakarunta da hadin guiwar sauran hukumomin tsaro sun ceto ‘yan makaranta 137 da aka sace a Kuriga da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

Daraktan yada labarai na rundunar, Manjo Janar Edward Buba, ya ce yaran da aka ceto sun hada da mata 76 da maza 61 da safiyar Lahadi 24 ga Maris, 2024, a wani wuri a jihar Zamfara.

  • An Sako Ɗaliban Makarantar Kuriga Da Aka Sace A Kaduna – Uba Sani
  • Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna

Idan ba a manta ba LEADERSHIP HAUSA a ranar 7 ga Maris, 2024 ta rawaito muku yadda wasu ‘yan ta’adda suka kai hari makarantar LEA Kuriga, karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, inda suka yi awon gaba da ‘yan makaranta 287.

Gwamnatin tarayya dai ta umurci sojoji da su tabbatar an dawo da yaran makaranta lafiya.

A baya LEADERSHIP ta kawo rahoto kan cewa an kubutar da daliban, a cewar gwamnan jihar Uba Sani, wanda ya sanar da farko game da ceto yaran ba tare da bayyana adadin wadanda abin ya shafa ba a safiyar yau Lahadi.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sai dai a cewar sanarwar ta hedikwatar tsaron Nijeriya ta cfurta ya saba da alkaluman farko na adadin daliban da sojojin suka ce sun yi nasarar kubutar da su.

“A ranar Lahadi, 24 ga Maris, 2024, sojojin da ke aiki tare daw hadin guiwar wasu hukumomi sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

“Wadanda aka yi garkuwa da su daga makarantar da ke Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

“Dalibai 137 da aka yi garkuwa da su sun hada da mata 76 da maza 61, an ceto su ne a jihar Zamfara kuma za a mika su ga gwamnatin jihar Kaduna,” inji Manjo Janar Buba.

Rundunar sojin ta ce za a ci gaba da kokarin har sai an gano ragowar mutanen da aka yi garkuwa da su da tabbatar da an kama ’yan ta’addar an yi musu an gurfanar da su gaban shari’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daliban makarantar KurigaKadunaSojojiYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci

Next Post

Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

7 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

23 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sojoji

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.