• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar tsaron Nijeriya, ta bayyana cewa dakarunta da hadin guiwar sauran hukumomin tsaro sun ceto ‘yan makaranta 137 da aka sace a Kuriga da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna.

Daraktan yada labarai na rundunar, Manjo Janar Edward Buba, ya ce yaran da aka ceto sun hada da mata 76 da maza 61 da safiyar Lahadi 24 ga Maris, 2024, a wani wuri a jihar Zamfara.

  • An Sako Ɗaliban Makarantar Kuriga Da Aka Sace A Kaduna – Uba Sani
  • Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna

Idan ba a manta ba LEADERSHIP HAUSA a ranar 7 ga Maris, 2024 ta rawaito muku yadda wasu ‘yan ta’adda suka kai hari makarantar LEA Kuriga, karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, inda suka yi awon gaba da ‘yan makaranta 287.

Gwamnatin tarayya dai ta umurci sojoji da su tabbatar an dawo da yaran makaranta lafiya.

A baya LEADERSHIP ta kawo rahoto kan cewa an kubutar da daliban, a cewar gwamnan jihar Uba Sani, wanda ya sanar da farko game da ceto yaran ba tare da bayyana adadin wadanda abin ya shafa ba a safiyar yau Lahadi.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Sai dai a cewar sanarwar ta hedikwatar tsaron Nijeriya ta cfurta ya saba da alkaluman farko na adadin daliban da sojojin suka ce sun yi nasarar kubutar da su.

“A ranar Lahadi, 24 ga Maris, 2024, sojojin da ke aiki tare daw hadin guiwar wasu hukumomi sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

“Wadanda aka yi garkuwa da su daga makarantar da ke Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

“Dalibai 137 da aka yi garkuwa da su sun hada da mata 76 da maza 61, an ceto su ne a jihar Zamfara kuma za a mika su ga gwamnatin jihar Kaduna,” inji Manjo Janar Buba.

Rundunar sojin ta ce za a ci gaba da kokarin har sai an gano ragowar mutanen da aka yi garkuwa da su da tabbatar da an kama ’yan ta’addar an yi musu an gurfanar da su gaban shari’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daliban makarantar KurigaKadunaSojojiYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci

Next Post

Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

4 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

5 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

8 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

9 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

9 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

14 hours ago
Next Post
Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

Buhun Taki Miliyan 2 Da Biliyan 100 Da CBN Ya Bayar Zai Daidaita Farashin Abinci -Kyari

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.