• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Musawa Da Matazu Za Su Amfana Da Tallafin Karatun Naira Miliyan 32,500 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Musawa

Ɗalibai ‘yan asalin ƙananan hukumomin Musawa da Matazu masu karatu a manyan makarantun gaba da sakandare zasu amfana da tallafi daga gidauniyar ɗan majalisar tarayya Hon. Abdullahi Aliyu (Talban Musawa).

Wannan tallafi dai kimanin ɗalibai 1,991 da suka fito da mazaɓu 21 da ake da su a ƙananan hukumomin Musawa da Matazu kuma waɗanda suke Karatu a manyan makarantun gaba da sakandare ne za su amfana da shi.

  • Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina
  • Wa Ya Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina?

Shugaban kwamitin ilimi na ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Ƙananan hukumomin Musawa, dakta Samaila Adamu Dangani, ya bayyana cewa wannan wani tallafi ne na gidauniya ɗan majalisar domin tallafawa iyaye da ɗalibai.

Ya ƙara da cewa kimanin ɗalibai 1,087 ne suka fito daga ƙaramar hukumar Musawa a ya yin da 808 suka fito daga ƙaramar hukumar Matazu kuma dukkan su an tantance su, kuma sun tsallake ƙa’idojin da aka shinfiɗa don cin gajiyar tallafin.

A cewarsa masu karatun digiri da babar difloma (HND) zasu samu tallafin naira dubu ashirin (20,000) sai kuma masu karatun NCE da ƙaramar difloma (ND) kowanensu zai samu tallafin dubu sha biyar (15,000).

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

“Ina son na yi amfani da wannan damar na sanar da al’umma cewa tun farko, mun samu adadin ɗalibai 2,364 amma da aka yi aikin tantancewa shi ne mutum 1,991 suka samu nasara kuma sune za su amfana da wannan tallafi” inji Ɗangani

Dakta Samaila Adamu Dangani ya yi ƙarin haske da cewa wannan tallafi bai nuna bambanci siyasa ba, in dai mutum ya cancanta ko daga wace jam’iyya yake zai amfana matsawar dai ɗan asalin ƙananan hukumomin Musawa da Matazu ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
Barista Batulu

Nada Mace Babbar Mai Shari’a A Kano Ya Kara Mana Kwarin Gwiwa - Barista Batulu

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.