ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
3 weeks ago
Majalisa

A bisa ga abin da aka kira rashin son kai a siyasance, dan majalisar tarayya da ke wakiltar Kebbe/Tambuwal, Honarabul Abdussamad Dasuki ya bayyana cewar ba zai sake tsayawa takarar majalisar wakilai a zaben 2027 ba, matakin da ya dauka na sadaukarwar kashin kai domin bai wa matasa dama. 

 

Dasuki, babban jigo a Majalisar Tarayya, wanda aka fara zabe da shi a majalisar dokoki ta jiha a 2011 ya ce, shawarar da ya yanke ta samo asali ne daga imanin cewar dimokuradiyyar Nijeriya dole ne ta canza domin karbar sabbin muryoyi masu cike da kuzari.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma
  • Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

“Nijeriyar da muke bukata za ta samu ne kawai ta hanyar sadaukarwa, ya ce “bayan tuntubar jama’a ta, jagoran mu, iyalai na da abu mafi muhimmanci zuciyata, na yanke shawarar ba zan sake tsayawa takarar kujerar majalisar wakilai a zaben 2027 ba.”

 

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Dasuki, wanda shine shugaban rikon kwarya na Shirin Makomar Matasa A Yanzu, wani shiri na hada matasa da harkokin siyasa da aka kaddamar a ranar 1 ga Oktoba, 2025 a Abuja, ya bayyana cewa sanarwar shirin na cewar kashi 70% na kujerun majalisar wakilai a zaben 2027 su kasance na ‘yan Nijeriya kasa da shekaru 40, ba kawai magana ce ta fafutuka ba, har ila yau kalubale ne ga shugabanni.

 

Matakin Dasuki ya kasance wani muhimmin lamari a farfajiyar siyasar Najeriya, inda ’yan siyasa kalilan ke ja da baya daga mukaman su. Sanarwar sa an fassara ta sosai a matsayin wakilcin  gwagwarmayar adalci tsakanin tsararraki wanda ya taimaka wajen jagoranta, wanda ke nufin rage gibin da ke tsakanin tsofaffi da matasa a shugabancin kasa.

 

Yayin da yake waiwayen tafiyar siyasarsa a tsawon shekaru 14 wadda ta hada da Majalisar Dokoki ta Jiha, Majalisar Wakilai ta Tarayya da Majalisar Zartarwa ta Jiha, Dasuki ya bayyana godiya ga mazabarsa, abokan aikinsa, da kuma ubangidan siyasarsa, tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal.

 

Ya ce “Duka babu yadda za a yi wadannan nasarorim su samu ba tare da cikakken goyon baya maras iyaka daga ubangidan siyasa ta ba, kuma jagora na Mai Girma Sanata Aminu Waziri Tambuwal (Mutawallen Sakkwato)

 

“Shugaba ne da ya ga baiwa a cikin wani matashi, ya tallafawa burina na siyasa, ya ba ni damar yin hidima a cikin majalisarsa. Har abada zan kasance mai godiya gare shi saboda amincewar da ya nuna a gareni, da kuma damar da ya bani na jagoranci da koyon darussa masu matukar muhimmanci.

 

“Ga mazaba ta, kun ba ni amincewar ku, kuma na dauke ta a matsayin alamar girmamawa. Ina neman goyon bayanku wajen tabbatar da wannan babban sauyi zuwa sabon babi. Tafiyar da ke gaba ba mai sauki ba ce, za mu fuskanci kalubale da jarrabawa, amma za mu iya shawo kan su idan muka hada kai bisa manufa daya, wato gina Nijeriya mafi kyau, karkashin jagorancin matasa masu kuzari, basira, da kwazo.

 

“Ga matasa babu wani sauran jira kuma! Babu wani sauran uzuri! Babu sauran shiru! Ku dauki matsayin ku. Ku tsayu da karfi. Ku karbi jagoranci da jarumta da gaskiya da hangen nesa. Ku gina mafi kyawun kyakkyawar makoma.” Ya fada cike da kwarin guiwa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana'o'i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.